Home Labarai Amurka za ta sayar wa Nijeriya makamai da kuɗinsu ya kai dala...

Amurka za ta sayar wa Nijeriya makamai da kuɗinsu ya kai dala miliyan 346

Ma’aikatar harkokin tsaron Amurkar ta ce gwamnatin kasar ta amince ta sayar wa Nijeriya makamai da kuɗinsu ya kai dala miliyan 346

gwamantin kasar ta ce makaman da za a sayar wa Najeriyar sun haɗa da manyan bama-bamai da kuma rokoki, wanda sayar da makaman zai ƙara inganta ɓangaren tsaron Najeriya da kuma taimakawa tsarin harkokin wajen ta a yankin kudu da Hamadar Saharar Afirka.

“Cikin makaman har da wasu rokoki na zamani sama da 5,000,” in ji sanarwar Washington.

A 2014 lokacin mulkin Barack Obama, Amurka ta ki amincewa ta sayar wa Najeriya wasu muggan makamai, bayan nuna damuwa kan zargin sojojin ƙasar da take hakkin ɗan’adam.

A lokacin, gwamnatin Najeriya ta yi ƙorafin cewa hakan na yin cikas a yaƙi da take yi da masu tayar da kayar baya a arewa maso gabashin kasar.

Har zuwa yau, Nijeriya na ci gaba da fuskantar matsalolin tsaro da suka haɗa da hare-hare da ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi ke kai wa da kuma ayyukan masu garkuwa da mutane a arewa maso yamma da kuma ƴan awaren Biafra a kudu maso gabashin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp