Home Labarai Amurka za ta sayar wa Nijeriya makamai da kuɗinsu ya kai dala...

Amurka za ta sayar wa Nijeriya makamai da kuɗinsu ya kai dala miliyan 346

Ma’aikatar harkokin tsaron Amurkar ta ce gwamnatin kasar ta amince ta sayar wa Nijeriya makamai da kuɗinsu ya kai dala miliyan 346

gwamantin kasar ta ce makaman da za a sayar wa Najeriyar sun haɗa da manyan bama-bamai da kuma rokoki, wanda sayar da makaman zai ƙara inganta ɓangaren tsaron Najeriya da kuma taimakawa tsarin harkokin wajen ta a yankin kudu da Hamadar Saharar Afirka.

“Cikin makaman har da wasu rokoki na zamani sama da 5,000,” in ji sanarwar Washington.

A 2014 lokacin mulkin Barack Obama, Amurka ta ki amincewa ta sayar wa Najeriya wasu muggan makamai, bayan nuna damuwa kan zargin sojojin ƙasar da take hakkin ɗan’adam.

A lokacin, gwamnatin Najeriya ta yi ƙorafin cewa hakan na yin cikas a yaƙi da take yi da masu tayar da kayar baya a arewa maso gabashin kasar.

Har zuwa yau, Nijeriya na ci gaba da fuskantar matsalolin tsaro da suka haɗa da hare-hare da ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi ke kai wa da kuma ayyukan masu garkuwa da mutane a arewa maso yamma da kuma ƴan awaren Biafra a kudu maso gabashin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp