Home General Gwamnonin PDP na taro a Zamfara

Gwamnonin PDP na taro a Zamfara

Gwamnonin jam’iyyar PDP a Najeriya na gudanar da wani taro a jihar Zamfara domin tattaunawa kan yunƙurinsu na “ɗaukar matakai masu muhimmanci”.

Taron zai fara ne daga yau Juma’a bayan hallarar gwamnonin, inda ake sa ran tattaunawa kan muhimman batutuwa a gobe Asabar.

A cikin sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa, taron na nufin tattauna muhimman batutuwan siyasa da gwamnonin ke fuskanta a halin yanzu.

PDP, wadda ita ce babbar jam’iyyar adawa a Najeriya na fuskantar ƙalubale na rikicin cikin gida da kuma ficewar wasu daga cikin manyan ƴaƴanta, ko dai zuwa jam’iyyar APC mai mulki ko kuma wadanda ke alaƙanta kansu da haɗakar ƴan adawa waɗanda suka tare a jam’iyyar ADC.

Hakan na faruwa ne gabanin babban zaɓen ƙasar na 2027. inda ƴan siyasa a kasar ke ci gaba da shiri, duk kuwa da gargadin da hukumar zaɓen ƙasar mai zaman kanta ta ƙasar ta yi kan fara harkokin siyasa gabanin lokaci.

A cikin sanarwar da gwamnan ya fitar ya ce “taron zai mayar da hankali kan batutuwan da suka shafi haɗin kan jam’iyyar da kuma shirin bunƙasa ci gaban jihohi, musamman a lokacin da jam’iyyar ke shirin gudanar da babban taronta na kasa a garin Ibadan, a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba, 2025.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp