Home General PDP ta zargi APC da yunkurin kawo tasgaro a Damukradiyya

PDP ta zargi APC da yunkurin kawo tasgaro a Damukradiyya

Jam’iyyar PDP a jihar Sokoto ta yi Allah-wadai da kamawa da tsare tsohon gwamnan, lamarin da ta ce jam’iyyar APC ce ke neman jefa dimokuraɗiyyar ƙasar cikin ruɗani.

A wata sanarwa sakataren watsa labaran PDP na jihar, Hassan Sahabi Sanyinnawal ya fitar, ya ce wannan na cikin yunƙurin cin zarafi da murƙushe jam’iyyun adawa a ƙasar.

Ya ce ana wannan kame-kamen ne “a daidai lokacin da aka fara ƙoƙarin samar da haɗakar jam’iyyun adawa a ƙasar domin fuskantar zaɓe mai zuwa,” in ji shi, sannan ya ƙara da cewa kamen ba zai hana komai ba wajen yunƙurin da suke yi na kawo sauyi ba.

“Jam’iyyarmu na kira ga hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa da ta daina zama karen farauta domin cin zarafin jam’iyyun adawa.

Tun da farko, Hukumar EFCC ce ta kama tare da tsare tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, bisa zarginsa da almundahanar kuɗi.

Rahotanni sun ce sanatan ya isa ofishin hukumar ne da kansa domin amsa gayyatar da aika masa a ranar Litinin, sannan ta riƙe shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp