Home General PDP ta zargi APC da yunkurin kawo tasgaro a Damukradiyya

PDP ta zargi APC da yunkurin kawo tasgaro a Damukradiyya

Jam’iyyar PDP a jihar Sokoto ta yi Allah-wadai da kamawa da tsare tsohon gwamnan, lamarin da ta ce jam’iyyar APC ce ke neman jefa dimokuraɗiyyar ƙasar cikin ruɗani.

A wata sanarwa sakataren watsa labaran PDP na jihar, Hassan Sahabi Sanyinnawal ya fitar, ya ce wannan na cikin yunƙurin cin zarafi da murƙushe jam’iyyun adawa a ƙasar.

Ya ce ana wannan kame-kamen ne “a daidai lokacin da aka fara ƙoƙarin samar da haɗakar jam’iyyun adawa a ƙasar domin fuskantar zaɓe mai zuwa,” in ji shi, sannan ya ƙara da cewa kamen ba zai hana komai ba wajen yunƙurin da suke yi na kawo sauyi ba.

“Jam’iyyarmu na kira ga hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa da ta daina zama karen farauta domin cin zarafin jam’iyyun adawa.

Tun da farko, Hukumar EFCC ce ta kama tare da tsare tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, bisa zarginsa da almundahanar kuɗi.

Rahotanni sun ce sanatan ya isa ofishin hukumar ne da kansa domin amsa gayyatar da aika masa a ranar Litinin, sannan ta riƙe shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp