Home Labarai Hukumar NIS na shirin kafa shingen bincike a mashigar jihar Kano

Hukumar NIS na shirin kafa shingen bincike a mashigar jihar Kano

Hukumar lura da shige da fice ta Nijeriya NIS ta bukaci jami’anta da su sake zage dantse gami da inganta ayyukan su.

Shugabar hukumar CSI Kemi Nanna Nandap ce ta bayyana hakan yayin taron bikin daga likkafar jami’an hukumar 450 a shalkwatar hukumar dake jihar Kano.

CSI Nandap wadda ta sami wakilcin shugaban hukumar reshen jihar Kano Ibrahim Muhammad Abubakar lafiya ta bayyana muhimmanci Karin girman gami da sake inganta ayyukan hukumar ga jami’an

Abubakar lafiya ya kara da cewa hukumar ta yi wannan Karin girma ne ga Jami’an saboda hazaka da mayar da hankulansu akan aiki, ba wai dan sun fi kowa bane.

“Wannan Karin girma muka fada musu akan cewa, bawai ko sun fi wasu bane saboda hazakar su ne da kuma kwarewar su a wurin aiki, da kuma suka ci jarrabawa shine Allah ya basu wannan matsayin da yanzu suke kai”

“Muna yi musu murna, muna kuma jan hankalin su da su sake daure damararsu, kasancewar akwai Jan aiki a gabansu a wannan ma’aikata ta shige da fice.

Haka kuma shugaban hukumar ya sake zaburar da jami’an hukumar wajen sanya idanu, don magance harkokin safarar mutane dake addabar nahiyar Afirka da ma kasa baki daya.

Inda ya ce hukumar ta shirya tsaf domin sake fadada ayyukanta a kananan hukumomin jihar Kano 44 don kawo karshen wannan matsala.

“Yanzu haka muna da wani shiri da muke jiran umarni daga sama, domin fara wani aiki kafa shingen bincike a dukkanin mashigar jihar kano da ko wacce kusurwa”

Yace sun dauki wannan mataki domin kada ma wadanda ake safarar a sami damar fita ko shigo da jihar Kano.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp