Home Labarai Hukumar NIS na shirin kafa shingen bincike a mashigar jihar Kano

Hukumar NIS na shirin kafa shingen bincike a mashigar jihar Kano

Hukumar lura da shige da fice ta Nijeriya NIS ta bukaci jami’anta da su sake zage dantse gami da inganta ayyukan su.

Shugabar hukumar CSI Kemi Nanna Nandap ce ta bayyana hakan yayin taron bikin daga likkafar jami’an hukumar 450 a shalkwatar hukumar dake jihar Kano.

CSI Nandap wadda ta sami wakilcin shugaban hukumar reshen jihar Kano Ibrahim Muhammad Abubakar lafiya ta bayyana muhimmanci Karin girman gami da sake inganta ayyukan hukumar ga jami’an

Abubakar lafiya ya kara da cewa hukumar ta yi wannan Karin girma ne ga Jami’an saboda hazaka da mayar da hankulansu akan aiki, ba wai dan sun fi kowa bane.

“Wannan Karin girma muka fada musu akan cewa, bawai ko sun fi wasu bane saboda hazakar su ne da kuma kwarewar su a wurin aiki, da kuma suka ci jarrabawa shine Allah ya basu wannan matsayin da yanzu suke kai”

“Muna yi musu murna, muna kuma jan hankalin su da su sake daure damararsu, kasancewar akwai Jan aiki a gabansu a wannan ma’aikata ta shige da fice.

Haka kuma shugaban hukumar ya sake zaburar da jami’an hukumar wajen sanya idanu, don magance harkokin safarar mutane dake addabar nahiyar Afirka da ma kasa baki daya.

Inda ya ce hukumar ta shirya tsaf domin sake fadada ayyukanta a kananan hukumomin jihar Kano 44 don kawo karshen wannan matsala.

“Yanzu haka muna da wani shiri da muke jiran umarni daga sama, domin fara wani aiki kafa shingen bincike a dukkanin mashigar jihar kano da ko wacce kusurwa”

Yace sun dauki wannan mataki domin kada ma wadanda ake safarar a sami damar fita ko shigo da jihar Kano.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp