Home General Ƴan ta’addar da suka tsere daga Zamfara na yi wa Kano barazana

Ƴan ta’addar da suka tsere daga Zamfara na yi wa Kano barazana

Hukumomi a Najeriya sun tsaurara matakan tsaro da kuma sa-ido sosai a birnin Kano, bayan da wani rahoton da hukumomin tara bayan sirri suka gano cewa yanzu ɗimbin ƴan bindiga sun tsere daga Zamfara inda suke fakewa a cikin birnin wanda shi ne mafi girma a arewacin kasar.

Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP ne ya sanar da hakan, bayan da ya samo kwafin wasikar da hukumomin tara bayanan sirri daga Zamfara suka tura wa takwarorinsu da ke Kano.

A cewar AFP, tun a ranar Litinin da ta gabata ne aka gabatar wa gwamnan jihar Kano da wannan rahoto, da ke cewa mafi yawan ƴan bindigar tuni suka mallaki gidaje a cikin birnin Kano, yayin da wasu ke fakewa a unguwannin Rijiyar Zaki, Tudun Yola, Ja’en, Ɗorayi Babba, Rijiyar Lemo da kuma Ƴan Awaki.

Bisa ga dukan alamu, rahoton ya ce mafi yawan ƴan bindigar sun nemi mafaka a birnin Kano ne saboda tsanantar hare-hare da jami’an tsaro ke kai musu a cikin ƴan kwanakin nan, yayin da wasu suka mallaki gidajen tsawon shekaru a birnin a daidai lokacin da suke taimaka wa ƴan bindigar da ke gudanar da ayyukan tsagarenci a jihohin Zamfara, Katsina da kuma Kaduna.

Wasu majiyoyi biyu na tsaro, sun tabbatar wa Kamfanin Dillancin Labaran AFP da cewa rahoton ya shiga hannuwansu, yayin da wata majiyar ke cewa yanzu tana aiki tukuru domin zaƙulo su a cikin gaggawa.

To sai dai majiyar na cewa yanzu haka jami’an tsaro na aiki ne a asirce domin ka da jama’a su shiga hali na firgita.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp