Home Labarai Ku marawa Tinubu baya domin ya cimma burin sa – APC

Ku marawa Tinubu baya domin ya cimma burin sa – APC

APC

Jam’iyyar APC mai mulki ta shaida wa ‘yan adawa da su “binne tunanin sauya manufofin da gwamnatin shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu ke jagoranta, su marawa gwamnati baya wajen ganin ta cimma burin Shugaban kasa.

Jam’iyyar ta kuma yi watsi da ikirarin da ‘yan adawa suka yi na cewa ta tafka magudi a zaben gwamnan jihar Edo da aka yi ranar 21 ga watan Satumba a wani bangare na shirin kafa tsarin jam’iyya daya da mulkin kama-karya a kasar.

A ranar Alhamis din da ta gabata ne kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP ya yi zargin cewa jam’iyyar APC ta yi magudi a zaben Edo domin cimma shirinta na mayar da Najeriya kasa mai jam’iyya daya.

Da yake yiwa manema labarai jawabi bayan taron kwamitin amintattun jami’iyyar, da aka gudanar a sakatariyar jam’iyyar PDP ta kasa da ke Abuja, shugaban kwamitin, Sanata Adolphus Wabara, ya bayyana damuwarsa kan tabarbarewar zamantakewa da tattalin arzikin kasar, wanda ya dora alhakin hakan kan manufofin gwamnatin APC.

Sai dai da, yake mayar da martani kan zargin a ranar Juma’a, Daraktan Yada Labarai na jam’iyyar APC, Alhaji Bala Ibrahim, ya shaida wa Aminiya a wata tattaunawa ta wayar tarho cewa jam’iyya mai mulki ba ta da niyyar kawo cikas ga dimokradiyya.

Ibrahim ya ce, “Jam’iyyar APC a matsayinta na jam’iyya mai mulki ba ta da niyyar yi wa kasar nan duk wani abu da zai cutar da dimokradiyyar ta.

APC jam’iyya ce ta ci gaba; jam’iyya ce da ta fito domin kawo sauye-sauye da za su kawo wa al’umma ribar dimokuradiyya. Dimokuradiyya tana da fa’ida ne kawai idan aka samu adawa, amma adawar su zama mai ma’ana, ba barna ba.

“Kasar nan ta yi ta zubar da jini sosai a karkashin shugabancin PDP; sun yi wa kasar zagon kasa. Don haka ’yan Najeriya har yanzu suna kallo sun fara fahimtar ma’anar canji.”

Ya bukaci ‘yan adawa da su yi watsi da tunanin koma-bayan siyasa tare da marawa gwamnati baya.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp