Home Labarai Ku marawa Tinubu baya domin ya cimma burin sa – APC

Ku marawa Tinubu baya domin ya cimma burin sa – APC

APC

Jam’iyyar APC mai mulki ta shaida wa ‘yan adawa da su “binne tunanin sauya manufofin da gwamnatin shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu ke jagoranta, su marawa gwamnati baya wajen ganin ta cimma burin Shugaban kasa.

Jam’iyyar ta kuma yi watsi da ikirarin da ‘yan adawa suka yi na cewa ta tafka magudi a zaben gwamnan jihar Edo da aka yi ranar 21 ga watan Satumba a wani bangare na shirin kafa tsarin jam’iyya daya da mulkin kama-karya a kasar.

A ranar Alhamis din da ta gabata ne kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP ya yi zargin cewa jam’iyyar APC ta yi magudi a zaben Edo domin cimma shirinta na mayar da Najeriya kasa mai jam’iyya daya.

Da yake yiwa manema labarai jawabi bayan taron kwamitin amintattun jami’iyyar, da aka gudanar a sakatariyar jam’iyyar PDP ta kasa da ke Abuja, shugaban kwamitin, Sanata Adolphus Wabara, ya bayyana damuwarsa kan tabarbarewar zamantakewa da tattalin arzikin kasar, wanda ya dora alhakin hakan kan manufofin gwamnatin APC.

Sai dai da, yake mayar da martani kan zargin a ranar Juma’a, Daraktan Yada Labarai na jam’iyyar APC, Alhaji Bala Ibrahim, ya shaida wa Aminiya a wata tattaunawa ta wayar tarho cewa jam’iyya mai mulki ba ta da niyyar kawo cikas ga dimokradiyya.

Ibrahim ya ce, “Jam’iyyar APC a matsayinta na jam’iyya mai mulki ba ta da niyyar yi wa kasar nan duk wani abu da zai cutar da dimokradiyyar ta.

APC jam’iyya ce ta ci gaba; jam’iyya ce da ta fito domin kawo sauye-sauye da za su kawo wa al’umma ribar dimokuradiyya. Dimokuradiyya tana da fa’ida ne kawai idan aka samu adawa, amma adawar su zama mai ma’ana, ba barna ba.

“Kasar nan ta yi ta zubar da jini sosai a karkashin shugabancin PDP; sun yi wa kasar zagon kasa. Don haka ’yan Najeriya har yanzu suna kallo sun fara fahimtar ma’anar canji.”

Ya bukaci ‘yan adawa da su yi watsi da tunanin koma-bayan siyasa tare da marawa gwamnati baya.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp