Home General Ku dai na Tsinewa Shuwagabannin- Sarkin Musulmi

Ku dai na Tsinewa Shuwagabannin- Sarkin Musulmi

Mai alfarma Sarkin Sokoto, Alhaji Sa’ad Abubakar III ya yi kira ga ƴan Najeriya da cewa da su riƙa yi wa shugabannin ƙasar addu’a duk yanayin da ake ciki, kuma duk yanayin da ƙasar ke ciki.

Sultan ya yi wannan kiran ne a Jami’ar Ilorin a ranar Alhamis a lokacin da yake gabatar da jawabi a taron ƙaddamar da littafin da aka rubuta a kan shugaban hukumar JAMB Farfesa Is’haq Oloyede, wanda ya yi ritaya daga aikin jami’a kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Sultan ɗin ya ƙara cewa, “ku daina tsine wa shugabanni duk yadda abubuwa suka lalace, maimakon haka gara ku riƙa musu addu’a. Ku daina faɗin abubuwa marasa kyau a kansu. Duk lalacewar shugaba ku guji tsine masa,” in ji shi.

A nasa jawabin, ministan shari’a Lateef Fagbemi (SAN), wanda shi ne shugaban taron, kira ya yi ga ƴan Najeriya da su riƙa ƙarfafa wa shugabanninsu gwiwa.

“Ban ce babu matsala ba, amma da zarar kun fara ɓata ƙasarku a idon duniya, ban san me muke tuna wa duniya ba game da ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp