Home Labarai Kotu ta hana PDP tsige Damagun a matsayin shugaban riƙo

Kotu ta hana PDP tsige Damagun a matsayin shugaban riƙo

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da kwamitin amintattu BOT da majalisar ƙolinta daga cire Umar Damagun a matsayin shugaban riƙo na jam’iyyar.

Mai shari’a Peter Lifu ne ya bayar da umarnin a hukuncin da ya yanke, inda ya ce Damagun ne zai cigaba da zama shugaban jam’iyyar na riƙo har zuwa ranar da za a gudanar da babban taron jam’iyyar a watan Disamban 2025.

Alƙalin ya ce bisa la’akari da sashe na 42 da 47 da 67 na jam’iyyar, a babban taron jam’iyyar ne kawai za a zaɓan wani sabon shugaba, inda ya ce dole duk wani ɗan jam’iyyar ya yi biyayya ga kundin tsarin mulkin jam’iyyar.

Mai shari’a Lifu ya ƙara da cewa yanzu zangon shugabancin PDP na Arewa ne, inda ya ƙara da cewa tunda an zaɓi Damagun ne domin ƙarasa zangon mulkin Iyorchia Ayu wanda shi ma ɗan yankin ne, dole ya ƙarasa zangon.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp