Home Labarai An hallaka manoma huɗu a wani hari a Filato

An hallaka manoma huɗu a wani hari a Filato

'Yan Ta'adda

Rahotanni sun bayyana cewa an kashe wasu manoma huɗu tare da jikkata wasu biyar a wani hari da aka sake kai wa wurin hakar ma’adinai kusa da kauyukan Kuba da Maikatako da ke karamar hukumar Bokkos na jihar Filato.

Shugaban matasan yankin Butura, Sabastine Majit, shi ya tabbatar da faruwar lamarin a Jos ranar Asabar, inda ya ce an kai harin ne da misalin karfe na dare ranar Alhamis.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito shi yana cewa maharan sun tsere bayan kai harin, kafin isar jami’an tsaro.

“Wanna hari ya zo ne kwanaki huɗu bayan wani mummunan hari a kauyen Wumat, inda aka kashe mutum biyar ƴan gida ɗaya, ciki har da wata mata mai ciki,” in ji Sabastine.

Ya ce wannan hari shi ne na baya-bayan nan da ake kai wa al’ummomin yankin, wanda ya janyo mutuwar mutum 20 a cikin wata ɗaya kaɗai.

Ya ƙara da cewa wannan na cikin hare-hare da yawa da ake kai wa ƙananan hukumomin Barkin Ladi da Riyom da Bassa da Jos ta Arewa da kuma ta Kudu da Wase da kuma Mangu a baya-bayan nan, inda ake kashe mutane.

Sai dai babu wani ƙarin bayani daga rundunar ƴansandan jihar ta Filato kan wannan hari da aka kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp