Home Labarai An hallaka manoma huɗu a wani hari a Filato

An hallaka manoma huɗu a wani hari a Filato

'Yan Ta'adda

Rahotanni sun bayyana cewa an kashe wasu manoma huɗu tare da jikkata wasu biyar a wani hari da aka sake kai wa wurin hakar ma’adinai kusa da kauyukan Kuba da Maikatako da ke karamar hukumar Bokkos na jihar Filato.

Shugaban matasan yankin Butura, Sabastine Majit, shi ya tabbatar da faruwar lamarin a Jos ranar Asabar, inda ya ce an kai harin ne da misalin karfe na dare ranar Alhamis.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito shi yana cewa maharan sun tsere bayan kai harin, kafin isar jami’an tsaro.

“Wanna hari ya zo ne kwanaki huɗu bayan wani mummunan hari a kauyen Wumat, inda aka kashe mutum biyar ƴan gida ɗaya, ciki har da wata mata mai ciki,” in ji Sabastine.

Ya ce wannan hari shi ne na baya-bayan nan da ake kai wa al’ummomin yankin, wanda ya janyo mutuwar mutum 20 a cikin wata ɗaya kaɗai.

Ya ƙara da cewa wannan na cikin hare-hare da yawa da ake kai wa ƙananan hukumomin Barkin Ladi da Riyom da Bassa da Jos ta Arewa da kuma ta Kudu da Wase da kuma Mangu a baya-bayan nan, inda ake kashe mutane.

Sai dai babu wani ƙarin bayani daga rundunar ƴansandan jihar ta Filato kan wannan hari da aka kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp