Home Labarai An hallaka manoma huɗu a wani hari a Filato

An hallaka manoma huɗu a wani hari a Filato

'Yan Ta'adda

Rahotanni sun bayyana cewa an kashe wasu manoma huɗu tare da jikkata wasu biyar a wani hari da aka sake kai wa wurin hakar ma’adinai kusa da kauyukan Kuba da Maikatako da ke karamar hukumar Bokkos na jihar Filato.

Shugaban matasan yankin Butura, Sabastine Majit, shi ya tabbatar da faruwar lamarin a Jos ranar Asabar, inda ya ce an kai harin ne da misalin karfe na dare ranar Alhamis.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito shi yana cewa maharan sun tsere bayan kai harin, kafin isar jami’an tsaro.

“Wanna hari ya zo ne kwanaki huɗu bayan wani mummunan hari a kauyen Wumat, inda aka kashe mutum biyar ƴan gida ɗaya, ciki har da wata mata mai ciki,” in ji Sabastine.

Ya ce wannan hari shi ne na baya-bayan nan da ake kai wa al’ummomin yankin, wanda ya janyo mutuwar mutum 20 a cikin wata ɗaya kaɗai.

Ya ƙara da cewa wannan na cikin hare-hare da yawa da ake kai wa ƙananan hukumomin Barkin Ladi da Riyom da Bassa da Jos ta Arewa da kuma ta Kudu da Wase da kuma Mangu a baya-bayan nan, inda ake kashe mutane.

Sai dai babu wani ƙarin bayani daga rundunar ƴansandan jihar ta Filato kan wannan hari da aka kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp