Home Labarai Sanata Ndume ya bukaci Tinubu ya tausayawa ‘yan Nijeriya

Sanata Ndume ya bukaci Tinubu ya tausayawa ‘yan Nijeriya

Ɗan majalisar dattijan Najeriya mai wakiltar Borno ta kudu, Sanata Ali Ndume ya yi kira ga shugaba Bola Tinubu da ya rage farashin man fetur, inda ya ce ƴan Najeriya na cikin wahala.

Ndume ya bayyana haka ne yayin tattaunawa da manema labarai a Abuja, inda ya kuma ce ci gaba da ƙara farashin man fetur da abinci da kuma kayan amfani na yau da kullum na ƙara jefa ƴan Najeriya cikin kunci da wahala, musamman ma talakawa.

Tsohon mai tsawatarwa na majalisar ya ce wasu ɓata-gari cikin gwamnati na ƙoƙarin haddasa fitina tsakanin mutane da gwamnatin Tinubu ta hanyar ɓullo da tsare-tsare masu tsauri da kuma mara kyau maimakon shawo kan matsalar hauhawar farashi da kuma tashin kuɗin dala da ke ci gaba da kassara ƴan ƙasar.

“Wasu ne kawai ke son ɓata Tinubu a idon jama’a ta hanyar ɓullo da waɗannan tsare-tsare daga karshe kuma laifi ya koma kan shugaban.

“Ina kira ga shugaban ƙasa da ya daina kula waɗannan mutane da ke son kawo cikas ga gwamnatinsa.Halin kunci da mutanen ke sa ƴan Najeriya ba zai misaltu ba,” in ji Ndume.

Ya ce mutane na cikin matsanancin wahala musamman ma jihar sa ta Borno.

“Mutane na cikin matsi, akwai yunwa, ɓacin-rai da kuma fushi cikin al’umma,” in ji Sanatan.

Ya ce ya san shugaba Tinubu yana da manufa mai kyau ga ƴan Najeriya, sai dai wasu masu ba shi shawara ne ke son kassara ƴan ƙasar ta hanyar ba shi shawara mara amfani.

Sanata Ndume ya buƙaci shugaban ƙasar da ya duba batutuwan da zarar ya koma daga hutun da ya tafi da nufin shawo kan su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp