Home Taska Dole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali – Babban Hafsan Tsaro

Dole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali – Babban Hafsan Tsaro

Janar Olufemi Oluyede

Dole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali – Babban Hafsan Tsaro

 

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Olufemi Oluyede ya buƙaci dakarun tsaron ƙasar su ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ƴanbindiga a jihohin arewa maso yamma, inda ya nanata cewa dole a tabbatar Najeriya da ƴan Najeriya sun samu tsaro “ta kowane hali.”

Janar Oluyede ya bayyana haka a ziyarar da ya kai wa sojojin da suke aiki na musamman na Fansan Yamma a garin Gusau da ke jihar Zamfara.

“Saƙona a fayyace yake: dole dakaru su fita su bi ɓatagari har maɓoyarsu su kawo ƙarshensu. Dole mu tabbatar da tsaron Najeriya ta ko wane hali.”

Hafsan ya bayyana shirin rundunar tsaron Najeriya na kawo ƙarshen matsalolin ƴanbindiga a jihohin arewa ta yamma, inda ya ƙara da cewa idan aka cigaba da matsa wa ƴanbindigar lamba ne za a samu sauƙi da zaman lafiyar da ake buƙata.

Janar ɗin ya kuma yaba da ƙoƙarin gwamnatin jihar Zamfara da ƴan jihar bisa irin gudunmuwar da suke ba jami’an tsaro.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp