Home Taska Dole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali – Babban Hafsan Tsaro

Dole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali – Babban Hafsan Tsaro

Janar Olufemi Oluyede

Dole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali – Babban Hafsan Tsaro

 

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Olufemi Oluyede ya buƙaci dakarun tsaron ƙasar su ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ƴanbindiga a jihohin arewa maso yamma, inda ya nanata cewa dole a tabbatar Najeriya da ƴan Najeriya sun samu tsaro “ta kowane hali.”

Janar Oluyede ya bayyana haka a ziyarar da ya kai wa sojojin da suke aiki na musamman na Fansan Yamma a garin Gusau da ke jihar Zamfara.

“Saƙona a fayyace yake: dole dakaru su fita su bi ɓatagari har maɓoyarsu su kawo ƙarshensu. Dole mu tabbatar da tsaron Najeriya ta ko wane hali.”

Hafsan ya bayyana shirin rundunar tsaron Najeriya na kawo ƙarshen matsalolin ƴanbindiga a jihohin arewa ta yamma, inda ya ƙara da cewa idan aka cigaba da matsa wa ƴanbindigar lamba ne za a samu sauƙi da zaman lafiyar da ake buƙata.

Janar ɗin ya kuma yaba da ƙoƙarin gwamnatin jihar Zamfara da ƴan jihar bisa irin gudunmuwar da suke ba jami’an tsaro.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp