Home Taska ‘Yan Daba Sun Farmaki Kasuwar Sayar da Wayoyin Hannu a Jihar Kano

‘Yan Daba Sun Farmaki Kasuwar Sayar da Wayoyin Hannu a Jihar Kano

Farm Center

‘Yan Daba Sun Farmaki Kasuwar Sayar da Wayoyin Hannu a Jihar Kano

 

Kano, Nigeria – Wasu da ake zargin ‘yan daba ne sun kai hari fitacciyar kasuwar sayar da wayoyin hannu watau Farm Center da ke cikin kwaryar birnin jihar Kano.

Rahotanni da ba a tabbatar da su ba, sun nuna cewa wasu daga cikin maharan sun fito ne daga wani taron siyasa da aka gudanar , sai dai babu wata sanarwa a hukumance da ta tabbatar da hakan.

Matakin da jami’an tsaro suka dauka

Daga bisani, jami’an ‘yan sanda sun isa wurin, inda suka tarwatsa maharan tare da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasuwar ta Farm Center.

Wata majiya a kasuwar ta shaidawa Daily Nigerian Hausa cewa, ana zargin ƴan daban sun halarci wani taron siyasa da aka yi a yankin, kafin su farmaki wajen siyar da wayar da ke Yoyo Plaza.

Majiyar ta kara da cewa, ƴan daban sun daka wawa tare da kai sara ga ƴan kasuwar dake tsaka da ciniki, haka kuma, sun dinga kwacewa mutane wayoyinsu a kan hanya.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu tabbacin mutuwar kowa, amma an ce mutane da dama sun samu raunuka Hukumomi ba su fitar da wata sanarwa a hukumance ba tukuna, yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp