Home Taska ‘Yan Daba Sun Farmaki Kasuwar Sayar da Wayoyin Hannu a Jihar Kano

‘Yan Daba Sun Farmaki Kasuwar Sayar da Wayoyin Hannu a Jihar Kano

Farm Center

‘Yan Daba Sun Farmaki Kasuwar Sayar da Wayoyin Hannu a Jihar Kano

 

Kano, Nigeria – Wasu da ake zargin ‘yan daba ne sun kai hari fitacciyar kasuwar sayar da wayoyin hannu watau Farm Center da ke cikin kwaryar birnin jihar Kano.

Rahotanni da ba a tabbatar da su ba, sun nuna cewa wasu daga cikin maharan sun fito ne daga wani taron siyasa da aka gudanar , sai dai babu wata sanarwa a hukumance da ta tabbatar da hakan.

Matakin da jami’an tsaro suka dauka

Daga bisani, jami’an ‘yan sanda sun isa wurin, inda suka tarwatsa maharan tare da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasuwar ta Farm Center.

Wata majiya a kasuwar ta shaidawa Daily Nigerian Hausa cewa, ana zargin ƴan daban sun halarci wani taron siyasa da aka yi a yankin, kafin su farmaki wajen siyar da wayar da ke Yoyo Plaza.

Majiyar ta kara da cewa, ƴan daban sun daka wawa tare da kai sara ga ƴan kasuwar dake tsaka da ciniki, haka kuma, sun dinga kwacewa mutane wayoyinsu a kan hanya.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu tabbacin mutuwar kowa, amma an ce mutane da dama sun samu raunuka Hukumomi ba su fitar da wata sanarwa a hukumance ba tukuna, yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp