Home Taska Ƙungiyar MURIC na Zargin Gwamnatin Najeriya da Nuna wa Musulmai Bambanci

Ƙungiyar MURIC na Zargin Gwamnatin Najeriya da Nuna wa Musulmai Bambanci

Tinubu MURIC

Ƙungiyar MURIC na Zargin Gwamnatin Najeriya da Nuna wa Musulmai Bambanci

 

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Musulmi (MURIC) ta zargi gwamnatin Najeriya da nuna fifiko tsakanin Musulmai da Kiristoci a ƙasar.

Wannan na zuwa ne bayan da rahotanni suka ce gwamnatin tare da ƙungiyar Kiristoci (CAN), sun ƙaddamar gina wani katafaren coci da za kashe wa naira biliyan 25 a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, babban birnin ƙasar.

A wata sanarwa da MURIC ta aike wa BBC, shugaban ƙungiyar Farfesa Ishaq Akintola ya kuma nuna takaici kan yadda gwamnatin ta tallafa wa waɗanda rikici ya shafa a jihar Filato da naira biliyan 2, ba tare da ta yi irin hakan a jihohin Sakkwato, Borno, Kebbi da Zamfara ba, da su ma suke fama da matsalolin tsaro.

“Ya kamata gwamnatin tarayya ta yi bayanin dalilin da ya sa ake nuna wannan fifiko. Musulmai a Najeriya ba su cancanci haka ba…,” in ji sanarwar.

Ƙungiyar ta kuma buƙaci gwamnatin Najeriyar ta ware irin waɗannan kuɗaɗe na kimanin naira biliyan 25, da kuma fili ga Musulman ƙasar domin su ma su gina katafaren masallaci a filin jirgin.

Sanarwar ta ƙara da cewa: “Wannan haƙƙin mu ne. Kuma ya kamata a ba mu.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp