Home Taska Gwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram

Gwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram

Mai Mala Buni

Gwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram

Gwamnatin Yobe ta yi alƙawarin sake tumke ɗamarar kawo ƙarshen sabbin hare-haren ‘yan ta’addan Boko Haram da haramtaccen harajin da suke ƙaƙaba wa manoma a faɗin jihar.

Mataimakin gwamnan jihar Idi Barde Gubana ne ya bayyana hakan a zaman kwamitin zartaswa na jihar karo na 18 da aka gudanar a ranar Laraba.

Gubana wanda ya wakilci Gwamna Mai Mala Buni ya ce taron gaggawar na zuwa ne bayan sabbin hare-hare da ’yan ta’adda suka kai sansanonin soji, wanda ya ce ba ƙaramar barazana ce ga zaman lafiyar jihar ba.

Ya kuma bayyana damuwa kan hare-haren ‘yan ta’addan a garuruwan Yunusari, Geidam, da Tarmuwa, inda suke tilasta wa mutane da kuma manoma biyansu jangali da haraji.

“Idan za ku iya tunawa a baya-bayan nan an samu hare-hare da wasu sansanin sojojinmu da dama.

“Haka kuma ana tilasta wa mutanenmu biyan jangali da haraji musamman a ƙananan hukumomin Yunusari, Geidam, da Tarmuwa da sauransu.

“Mun taru a nan ne domin tattauna yadda za mu tabbatar mun kawo ƙarshen miyagun nan domin babban aikin gwamnati shi ne kare rayuka da dukiyoyin jama’a.”

Gubana ya kuma ce duk da cewa jihar ta samu zaman lafiya na ɗan wani lokaci, hare-haren bayan nan na buƙatar jajircewar jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki.

Ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan sojoji da ‘yan sandan da aka kashe a harin makarantar horas da wasan kwaikwayo ta Arewa maso Gabas da ke garin Buni Yadi a Ƙaramar Hukumar Gujba.

Aminiya ta rawaito cewa harin na ranar Juma’a ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla sojoji da ‘yan sanda 36.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp