Home Taska Gwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram

Gwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram

Mai Mala Buni

Gwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram

Gwamnatin Yobe ta yi alƙawarin sake tumke ɗamarar kawo ƙarshen sabbin hare-haren ‘yan ta’addan Boko Haram da haramtaccen harajin da suke ƙaƙaba wa manoma a faɗin jihar.

Mataimakin gwamnan jihar Idi Barde Gubana ne ya bayyana hakan a zaman kwamitin zartaswa na jihar karo na 18 da aka gudanar a ranar Laraba.

Gubana wanda ya wakilci Gwamna Mai Mala Buni ya ce taron gaggawar na zuwa ne bayan sabbin hare-hare da ’yan ta’adda suka kai sansanonin soji, wanda ya ce ba ƙaramar barazana ce ga zaman lafiyar jihar ba.

Ya kuma bayyana damuwa kan hare-haren ‘yan ta’addan a garuruwan Yunusari, Geidam, da Tarmuwa, inda suke tilasta wa mutane da kuma manoma biyansu jangali da haraji.

“Idan za ku iya tunawa a baya-bayan nan an samu hare-hare da wasu sansanin sojojinmu da dama.

“Haka kuma ana tilasta wa mutanenmu biyan jangali da haraji musamman a ƙananan hukumomin Yunusari, Geidam, da Tarmuwa da sauransu.

“Mun taru a nan ne domin tattauna yadda za mu tabbatar mun kawo ƙarshen miyagun nan domin babban aikin gwamnati shi ne kare rayuka da dukiyoyin jama’a.”

Gubana ya kuma ce duk da cewa jihar ta samu zaman lafiya na ɗan wani lokaci, hare-haren bayan nan na buƙatar jajircewar jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki.

Ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan sojoji da ‘yan sandan da aka kashe a harin makarantar horas da wasan kwaikwayo ta Arewa maso Gabas da ke garin Buni Yadi a Ƙaramar Hukumar Gujba.

Aminiya ta rawaito cewa harin na ranar Juma’a ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla sojoji da ‘yan sanda 36.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp