Home Taska Gwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram

Gwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram

Mai Mala Buni

Gwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram

Gwamnatin Yobe ta yi alƙawarin sake tumke ɗamarar kawo ƙarshen sabbin hare-haren ‘yan ta’addan Boko Haram da haramtaccen harajin da suke ƙaƙaba wa manoma a faɗin jihar.

Mataimakin gwamnan jihar Idi Barde Gubana ne ya bayyana hakan a zaman kwamitin zartaswa na jihar karo na 18 da aka gudanar a ranar Laraba.

Gubana wanda ya wakilci Gwamna Mai Mala Buni ya ce taron gaggawar na zuwa ne bayan sabbin hare-hare da ’yan ta’adda suka kai sansanonin soji, wanda ya ce ba ƙaramar barazana ce ga zaman lafiyar jihar ba.

Ya kuma bayyana damuwa kan hare-haren ‘yan ta’addan a garuruwan Yunusari, Geidam, da Tarmuwa, inda suke tilasta wa mutane da kuma manoma biyansu jangali da haraji.

“Idan za ku iya tunawa a baya-bayan nan an samu hare-hare da wasu sansanin sojojinmu da dama.

“Haka kuma ana tilasta wa mutanenmu biyan jangali da haraji musamman a ƙananan hukumomin Yunusari, Geidam, da Tarmuwa da sauransu.

“Mun taru a nan ne domin tattauna yadda za mu tabbatar mun kawo ƙarshen miyagun nan domin babban aikin gwamnati shi ne kare rayuka da dukiyoyin jama’a.”

Gubana ya kuma ce duk da cewa jihar ta samu zaman lafiya na ɗan wani lokaci, hare-haren bayan nan na buƙatar jajircewar jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki.

Ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan sojoji da ‘yan sandan da aka kashe a harin makarantar horas da wasan kwaikwayo ta Arewa maso Gabas da ke garin Buni Yadi a Ƙaramar Hukumar Gujba.

Aminiya ta rawaito cewa harin na ranar Juma’a ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla sojoji da ‘yan sanda 36.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp