Gwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
Gwamnatin Yobe ta yi alƙawarin sake tumke ɗamarar kawo ƙarshen sabbin hare-haren ‘yan ta’addan Boko Haram da haramtaccen harajin da suke ƙaƙaba wa manoma a faɗin jihar.
Mataimakin gwamnan jihar Idi Barde Gubana ne ya bayyana hakan a zaman kwamitin zartaswa na jihar karo na 18 da aka gudanar a ranar Laraba.
Gubana wanda ya wakilci Gwamna Mai Mala Buni ya ce taron gaggawar na zuwa ne bayan sabbin hare-hare da ’yan ta’adda suka kai sansanonin soji, wanda ya ce ba ƙaramar barazana ce ga zaman lafiyar jihar ba.
Ya kuma bayyana damuwa kan hare-haren ‘yan ta’addan a garuruwan Yunusari, Geidam, da Tarmuwa, inda suke tilasta wa mutane da kuma manoma biyansu jangali da haraji.
Read Also:
“Idan za ku iya tunawa a baya-bayan nan an samu hare-hare da wasu sansanin sojojinmu da dama.
“Haka kuma ana tilasta wa mutanenmu biyan jangali da haraji musamman a ƙananan hukumomin Yunusari, Geidam, da Tarmuwa da sauransu.
“Mun taru a nan ne domin tattauna yadda za mu tabbatar mun kawo ƙarshen miyagun nan domin babban aikin gwamnati shi ne kare rayuka da dukiyoyin jama’a.”
Gubana ya kuma ce duk da cewa jihar ta samu zaman lafiya na ɗan wani lokaci, hare-haren bayan nan na buƙatar jajircewar jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki.
Ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan sojoji da ‘yan sandan da aka kashe a harin makarantar horas da wasan kwaikwayo ta Arewa maso Gabas da ke garin Buni Yadi a Ƙaramar Hukumar Gujba.
Aminiya ta rawaito cewa harin na ranar Juma’a ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla sojoji da ‘yan sanda 36.










