Home Taska Bisa Kuskure: Sojojin Najeriya Sun Kashe Yara 7 Tare da Jikkata 5

Bisa Kuskure: Sojojin Najeriya Sun Kashe Yara 7 Tare da Jikkata 5

Bisa Kuskure: Sojojin Najeriya Sun Kashe Yara 7 Tare da Jikkata 5

 

Sojojin Najeriya sun yi kuskuren kashe yara bakwai tare da jikkata wasu biyar a wani harin sama da suka kai a yankin Maradi na Jamhuriyyar Nijar, kamar yadda gwamman yankin ya shaida wa kamfanin dillacin labaran Faransa.

Gwamnan Maradi Chaibou Aboubacar, ya ce hare-haren sama da sojojin Najeriya suka kai ya rutsa da yara a ƙauyen Nachade a ranar Juma’a.

Gwamnan ya ce suna tunanin sojojin Najeriya sun yi kuskuren kisan yaran ne a ƙoƙarin kai wa ‘yan bindiga a yankunan kan iyaka hari.

Babu dai wata sanarwa daga rundunar sojin Najeriya game da al’amarin.

Gwamnan Maradi ya ce lamarin ya shafi yara ne guda 12, kuma bakwai daga cikin sun mutu yayin da biyar ska jikkata.

A cewar gwamnan, harin ya rutsa da yaran ne suna cikin wasa yayin da iyayensu ke hidimar biki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp