Home Taska Rikicin Rasha da Ukraine: Kasar Burtaniya ta Daskarar da Kadarorin Mai Kungiyar...

Rikicin Rasha da Ukraine: Kasar Burtaniya ta Daskarar da Kadarorin Mai Kungiyar Kwallon Kafa ta Chelsea Roman Abramovich

Rikicin Rasha da Ukraine: Kasar Burtaniya ta Daskarar da Kadarorin Mai Kungiyar Kwallon Kafa ta Chelsea Roman Abramovich

Yayin da kasashen duniya ke ci gaba da kakaba takunkumi kan gwamnatin Putin da magoya bayansa, Burtaniya ta sake daukar mataki.

Ta sanya takunkumi kan mamallakin kungiyar kwallon kafa ta Chelsea tare da bayyana shi a matsayin dan tsagin Putin.

Wannan na zuwa ne lokacin da kasar Ukraine ke ci gaba da fuskantar hare-haren bama-bamai daga kasar Rasha.

Kasar Burtaniya ta daskarar da kadarorin mai kungiyar kwallon kafa ta Chelsea Roman Abramovich, kana ta sanya haramcin mu’amala da daidaikun mutane da ‘yan kasuwa na Burtaniya, da dokar hana zirga-zirga duk dai akansa.

Sky Sports ta rahoto Firayim Ministan Burtaniya, Boris Johnson yana cewa:

“Ba zai yiwu a samar da mafaka ga wadanda suka goyi bayan mummunan harin da Putin ya kai wa Ukraine ba.”

Hakazalika, ya kara da cewa:

“Takunkumin na yau shine mataki na baya-bayan nan na goyon bayan da Birtaniya ke baiwa al’ummar Ukraine ba tare da kakkautawa ba.

“Ba za mu sassauta ba wajen kuntatawa wadanda suka taimaka wajen kashe fararen hula, lalata asibitoci da kuma mamaye wasu ‘yan uwa ba bisa ka’ida ba.

Har ila yau, sakatariyar harkokin wajen Burtaniya Liz Truss ta ce:

“Takunkumin na yau ya sake nuna cewa ‘yan kama karya da masu cika aljihu da kudin kasa ba su da wani matsayi a cikin tattalin arzikinmu ko kuma al’ummarmu. Kusancinsu da Putin ke nuna suna da hannu wajen ta’addancin nasa.

“Jinin al’ummar Ukraine na hannunsu, ya kamata su rataye kawunansu saboda kunya.

“Goyon bayanmu ga Ukraine ba zai kassara ba. Ba za mu tsaya wata-wata ba a wannan aiki na kara matsi kan gwamnatin Putin da kuma kassara kudaden na’urar yakinsa na zalunci ba.

Karin bayani na nan tafe…

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp