Home Taska Rikicin Kasashen Biyu: Rasha ta Tabbatar da Kashe Jami’in Sojanta a Ukraine

Rikicin Kasashen Biyu: Rasha ta Tabbatar da Kashe Jami’in Sojanta a Ukraine

Rikicin Kasashen Biyu: Rasha ta Tabbatar da Kashe Jami’in Sojanta a Ukraine

Hukumomi a Rasha sun tabbatar da mutuwar mataimakin kwamandan a rundunar sojan ƙasar ta Black Sea Fleet, Kyaftin Andrei Paly, a filin yaƙi na garin Mariupol.

Har yanzu ana ci gaba da fafatawa a garin na Mariupol mai tashar jirgin ruwa.

Tun farko sakataren kwaliejin soja ne mai suna Konstantin Tsarenko ya tabbatar da mutuwar sojan a dandalin sada zumunta na Vkontakte (VK).

Gwamnan yankin Sevastopol, Mikhail Razvozhayev, ya faɗa cikin wani saƙon Telegram cewa “Andrei Nikolaevich ya zaɓi ya kare ƙasarmu a matsayin sana’arsa kuma ya rasu saboda mu zauna lafiya nan gaba”.

Rundunar sojan Ukraine ta yi iƙirarin kashe janar-janar na Rasha biyar tun bayan fara ɓarin wuta ranar 24 ga watan Fabarairu. Sai dai janar ɗaya ne kawai Rasha ta tabbaatar da mutuwarsa – Janar Andrei Sukhovetsky.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp