Home Taska ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Hedkwatar ‘Yan Sanda a Jahar Imo

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Hedkwatar ‘Yan Sanda a Jahar Imo

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Hedkwatar ‘Yan Sanda a Jahar Imo

 

Yan bindiga sun kai mummunan hari wata Hedkwatar yan sanda a Imo, mutane yankin sun tsorata sun yi takan su.

Wani mazaunin yankin ya ce Artabun da aka yi tsakankin dakarun yan sanda da maharan ya hargitsa mutane kamar duniya ce zata tashi.

Kakakin rundunar yan sanda na jihar Imo, Abattam, ya tabbatar da aukuwar lamarin, yace zai kara bincikawa.

Imo- Da safiyar Litinin, wasu ƴan bindiga sun farmaki hedkwatar yan sanda dake Otoko, ƙaramar hukumar Obowa a jihar Imo dake kudancin Najeriya.

Jaridar Punch ta tattaro cewa yan ta’addan sun bar jami’an yan sanda biyu kwance da rauni yayin harin.

Mazauna ƙauyen sun shaida wa manema labarai cewa maharan sun shigo da karfe 3:00 na dare, kuma sun kwashe dogon lokaci yayin harin.

Daily Trust ta rahoto Wani Mutumi ya ce:

“Bamu iya bacci ba da dare, ƙarar tashin makamai babban tashin hankali ne. Yayin da mutane da yawa suka tsere cikin jeji, wasu kuma sun fake a cikin gidajen su.”

“Hedkwatar yan sandan tana kan babbar hanyar Owerri-Umuahia, dakarun yan sanda sun tarbe su, suka fara artabu, komai ya ƙara dagulewa mutanen ƙauyen kai kace duniya ce zata tashi.”

“An yi kazamin musayar wuta da bamu taɓa gani ba, yan sanda biyu sun ji munanan raunuka, yanzu haka an gaggauta kai su Asibiti.”

Maharan sun kwashi kashinsu a hannu

Wata majiya ta daban ta bayyana cewa jami’an tsaro sun samu nasarar fatattakar yan bindiga kuma ba su samu damar shiga harabar hedkwatar yan sandan ba.

“Yan bindigan sun fuskanci turjiya daga yan sandan dake bakin aiki, ba su iya shiga harabar ba, an yi artabu mai muni. Yan sanda biyu sun jikkata, bansan halin da suke ciki ba.”

“Yanzu da nake magana da ku, an girke jami’an tsaro ta ko ina a yankin. Mutane a tsorace suke, kowa ya yi muƙus a cikin gida, abun dai ba daɗin ji.”

Kakakin rundunar yan sanda reshen jihar Imo, Micheal Abattam, da aka tuntuɓe shi yace, “Eh dagaske ne an kai hari,” amma ya yi alkawarin fitar da karin bayani daga baya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp