Home Labarai Tsaro: Rundunar Sojin Najeriya sun gano Naira Miliyan 60 da za a...

Tsaro: Rundunar Sojin Najeriya sun gano Naira Miliyan 60 da za a kai wa ‘Yan Bindiga Kudin fansa

Rundunar Sojin Najeriya ta ce Dakarunta sun bankado Naira Miliyan 60 da ake kokarin kai wa ‘yan ta’adda kudin fansar karbo wasu daga cikin wadanda ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su.

Haka kuma, dakarun sun yi nasarar kubutar da wasu mutane da aka yi garkuwa da su da suka hadar da mata da kananan yara.

Dakarun, wadanda suka hada da sojin sama da na kasa, sun kai ga cin karfin ‘yan bindigar. Inda suka bankado tare da kwato muggan makamai da bindiga kirar AK47, da albarusai da sauransu.

Jaridar PRNigeria ta rawaito cewar, cikin wadanda ake zargin zasu kai kudin fansar  akwai jami’in tsaro na farin kaya wato DSS.

Wani jami’in liken asiri ya shaidawa PRNigeria cewa dakarun sojin saman bataliya ta 271 a Birnin Gwarri, da Dakarun FOB na  Gwaska, sun kubutar da dimbin mutanen da aka yi garkuwa da su a yayin atisayen na hadin gwuiwa.

Jami’in ya ce: “An kwato zunzurutun kudi kimanin Naira Miliyan 60, Man Fetur da kuma muggan makamai, a yayin gudanar da aikin.

“Sauran kayayyakin da sojojin suka kwato daga hannun wadanda ake zargin sun hadar da Motoci, Bindigu kirar AK-47 Alburusai iri-iri da kuma wayoyin hannun.

“Za kuma a mika batun jami’an tsaron da suka hada da na DSS da ake zargi da kai kudin fansar ga ma’aikatar tsaron Najeriya, domin gudanar da bincike.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp