Home Labarai Gwamnan Kano zai koma Jam’iyyar APC

Gwamnan Kano zai koma Jam’iyyar APC

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, na shirin komawa jam’iyyar APC a ranar Litinin, 26 ga Janairu, 2026, bayan ya fice daga jam’iyyar NNPP a ranar Juma’ar da ta gabata.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya sanya wa hannu kuma aka raba manema labarai ranar Lahadi.

Idan Za a iya tunawa Gwamna Yusuf ya taba shiga jam’iyyar APC ne a shekarar 2014, lokacin da ya lashe zaɓen fidda gwani na jam’iyyar domin takarar Sanatan Kano ta Tsakiya, sai dai daga bisani ya janye wa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Sanarwar ta bayyana cewa bayan shafe shekaru yana harkokin siyasa a jam’iyyu daban-daban, ciki har da NNPP, inda a halin da ake ciki harkokin mulki, haɗin kan ƙasa da kuma buƙatar ci gaba sun sa ya yanke shawarar komawa APC, wadda ya bayyana a matsayin jam’iyya mai tsari da gogewa wajen tafiyar da mulkin dimokuraɗiyya.

Gwamna Yusuf ya ce komawarsa APC za ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin jihar da ta tarayya, da kawo ci gana jihar Kano .

Ya ƙara da cewa matakin zai taimaka wajen ƙarfafa kwanciyar hankali da haɗin kan siyasa a jihar.

A ranar Litinin, 26 ga Janairu, 2026, ana sa ran gwamnan zai yi rajistar shiga jam’iyyar APC a hukumance a Kano tare da mambobi 22 na Majalisar Dokokin Jihar Kano, mambobi takwas na Majalisar Wakilai da kuma shugabannin ƙananan hukumomi 44 na jihar.

Haka kuma ana sa ran zai ƙaddamar da shirin rajistar APC ta yanar gizo (e-registration) a faɗin jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp