Home Labarai Gwamnan Kano ya nada sabon mai ba shi shawara kan Siyasa

Gwamnan Kano ya nada sabon mai ba shi shawara kan Siyasa

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya cire Sunusi Surajo Kwankwaso daga mukamin mai ba shi shawara kan harkokin siyasa tare da maye gurbinsa da Mustapha Buhari Bakwana.

Hakan na cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran Gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Idan za’a iya tunawa Sunusi Surajo Kwankwaso ya bayyana cewa ya kai takardarsa ta ajiye aiki amma anki karbar, wanda ya ce hakan ce tasa a fito fili ya fadawa Duniya cewa ya ajiye mukamin nasa.

Sunusi Surajo Kwankwaso dai na daga cikin wadanda tun a tashin fari suka nuna cewa za su kasance tare da madugun Kwankwasiyya Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

Wannan dambarwar dai ta Sami asali ne tun lokacin da aka fara jita-jitar gwamnan Kano zai raba gari da ubangisansa na Siyasa Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

Bakwana dai ya taba rike wannan mukamin lokacin mulkin Dr. Abdullahi Umar Ganduje yana gwamnan Kano.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp