Home Labarai Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da yunƙurin juyin mulki a watan Oktoban...

Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da yunƙurin juyin mulki a watan Oktoban bara

Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da fuskantar yunƙurin juyin mulki ga gwamnatin ƙasar a kwanakin baya, wanda ta ce ta gano hakan ne bayan tsananta bincike kan wasu jami’anta da ta zarga da rashin ɗa’a inda sakamako ya tabbatar da cewa tabbas sun yi shirin kifar da gwamnatin ƙasar.

Tun a watan Oktoban 2025 ne, shalkwatar tsaron Najeriyar ta sanar da kame wasu manyan sojoji 16 bayan zarginsu da saɓa dokokin aiki, kodayake a wancan lokaci ta ƙi amsa zargin cewa sun yi shirin kifar da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ne.

A wancan lokaci wata kafar labarai a Najeriyar ta ruwaito cewa sashen tattara bayanan sirri na Najeriyar ya kame Sojojin masu muƙamai daga kyaftin zuwa Birgediya Janar su 16 lokacin da suke gudanar da wani taron sirri kan shirin kifar da gwamnati.

Kafar a wancan lokaci ta alaƙanta matakin soke faretin ranar 1 ga watan Oktoba da yunƙurin juyin mulkin, sai dai a wancan lokaci daraktan yaɗa labarai na shalkwatar Birgediya Tukur Gusau ya yi watsi da zargin wanda ya ce yunƙuri ne na haddasa yamutsi a tsakanin jama’ar ƙasar.

Sai dai da ya ke ƙarin haske kan lamarin a wannan Litinin, Manjo Janar Sama’ila Uba ya ce bayan dogon bincike irin na Soji kan Jami’an, ya tabbata suna kitsa shirin kifar da gwamnatin ta Najeriya.

A cewar Manjo Sama’ila Uba, mutanen su 16 za su gurfana don amsa tuhuma kan wannan zargi bisa tanadin dokokin aikin Soji na Najeriya, yayinda ya ce za a yi hukuncin ne a fayyace bisa tsantsar gaskiya da adalci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp