Home Labarai Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da yunƙurin juyin mulki a watan Oktoban...

Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da yunƙurin juyin mulki a watan Oktoban bara

Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da fuskantar yunƙurin juyin mulki ga gwamnatin ƙasar a kwanakin baya, wanda ta ce ta gano hakan ne bayan tsananta bincike kan wasu jami’anta da ta zarga da rashin ɗa’a inda sakamako ya tabbatar da cewa tabbas sun yi shirin kifar da gwamnatin ƙasar.

Tun a watan Oktoban 2025 ne, shalkwatar tsaron Najeriyar ta sanar da kame wasu manyan sojoji 16 bayan zarginsu da saɓa dokokin aiki, kodayake a wancan lokaci ta ƙi amsa zargin cewa sun yi shirin kifar da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ne.

A wancan lokaci wata kafar labarai a Najeriyar ta ruwaito cewa sashen tattara bayanan sirri na Najeriyar ya kame Sojojin masu muƙamai daga kyaftin zuwa Birgediya Janar su 16 lokacin da suke gudanar da wani taron sirri kan shirin kifar da gwamnati.

Kafar a wancan lokaci ta alaƙanta matakin soke faretin ranar 1 ga watan Oktoba da yunƙurin juyin mulkin, sai dai a wancan lokaci daraktan yaɗa labarai na shalkwatar Birgediya Tukur Gusau ya yi watsi da zargin wanda ya ce yunƙuri ne na haddasa yamutsi a tsakanin jama’ar ƙasar.

Sai dai da ya ke ƙarin haske kan lamarin a wannan Litinin, Manjo Janar Sama’ila Uba ya ce bayan dogon bincike irin na Soji kan Jami’an, ya tabbata suna kitsa shirin kifar da gwamnatin ta Najeriya.

A cewar Manjo Sama’ila Uba, mutanen su 16 za su gurfana don amsa tuhuma kan wannan zargi bisa tanadin dokokin aikin Soji na Najeriya, yayinda ya ce za a yi hukuncin ne a fayyace bisa tsantsar gaskiya da adalci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp