Home Labarai Ana tsammanin haifar jarirai dubu 700 cikin shekarar 2026 a Kano –...

Ana tsammanin haifar jarirai dubu 700 cikin shekarar 2026 a Kano – Gwamnati

Wasu alƙaluma da gwamnatin jihar Kano ta fitar ya nuna cewa jihar na tsammanin samun jarirai sabbin haihuwa aƙalla dubu 600 zuwa 700 da za a haifa cikin shekarar da muke ta 2026.

Alƙaluman wanda shugaban hukumar kula da asibitoci na jihar Dr Mansur Mudi Nagoda ya sanar na zuwa a dai dai lokacin da jihar ta Kano mafi yawan jama’a a yankin arewacin Najeriyar ke ganin ƙaruwar yawan jama’a.

Wasu bayanan baya-bayan nan sun nuna yadda yawan jama’ar jihar Kanon ya ƙaru da kashi 3.5.

A jawabinsa yayin bikin yaye ɗalibai na kwalejin kimiyya da Fasaha ta Sardauna da ke jihar, Dr Nagode ya ce duk da yawan jama’ar jihar akwai kuma tarin ƙalubalen lafiya da ya dabaibaye al’umma wanda ke nuna buƙatar jami’an lafiya don bayar da kulawa.

Dr Nagoda, ya yi gargaɗin cewa adadin jami’an lafiyar da jihar ke da su sunyi matuƙar kaɗan ga yawan al’ummarta, lura da yadda jama’ar ke ci gaba da ƙaruwa a kodayaushe.

A cewar shugaban hukumar kula da asibitocin na jihar Kano, yanzu haka jihar na fuskantar ƙarancin jami’an lafiya aƙalla dubu 4.

Dr Nagoda ya kuma roƙi makarantar horar da ɗaliban jinya da sauran ɓangarorin kiwon lafiya da su mayar da hankali wajen bayar da horo a aikace don ganin ɗaliban sun samu ƙwarewar da ta kamata wajen bayar da gudunmawa a cikin al’umma.

Akwai bayanan da ke nuna cewa jihar ta Kano na shirin ɗaukar sabbin jami’an lafiya zuwa wasu yankuna da basa samun kulawar da ta kamata ciki har da ƙananan hukumomin Doguwa da Rogo da Sumaila.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp