Home Labarai Matatar man Ɗangote ta ƙara farashin man fetur da naira 100

Matatar man Ɗangote ta ƙara farashin man fetur da naira 100

Matatar Man Ɗangote ta sanar da ƙarin farashin naira 100 kan kowacce litar man fetur guda inda a yanzu ta sanar da cewa za ta koma sayar da man akan farashinj naira 799.

Tun daga ranar 12 ga watan Disamban bara matatar ke sayar da kowacce litar man guda kan farashin naira 699 sai dai a wata sanarwa da ta fitar a jiya Litinin, ta ce farashin ya sauya nan ta ke.

Sanarwar matatar ta ce gidajen manta na MRS za su koma sayar da kowacce lita guda a farashin naira 839 daga naira 739 da suke sayarwa a baya.

Sanarwar ta Ɗangote ta ce tun farko an zaftare farashin ne saboda bukukuwan Kirsimati da sabuwar shekara, kuma bayan ƙarƙarewar wannan bukukuwa farashin zai dawo yadda ya ke a baya.

Matatar ta jaddada cewa za ta ci gaba da aiki tuƙuri wajen daidaita farashin man tare da tabbatar da wadatuwarsa a sassan ƙasar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp