Home Labarai Matatar man Ɗangote ta ƙara farashin man fetur da naira 100

Matatar man Ɗangote ta ƙara farashin man fetur da naira 100

Matatar Dangote

Matatar Man Ɗangote ta sanar da ƙarin farashin naira 100 kan kowacce litar man fetur guda inda a yanzu ta sanar da cewa za ta koma sayar da man akan farashinj naira 799.

Tun daga ranar 12 ga watan Disamban bara matatar ke sayar da kowacce litar man guda kan farashin naira 699 sai dai a wata sanarwa da ta fitar a jiya Litinin, ta ce farashin ya sauya nan ta ke.

Sanarwar matatar ta ce gidajen manta na MRS za su koma sayar da kowacce lita guda a farashin naira 839 daga naira 739 da suke sayarwa a baya.

Sanarwar ta Ɗangote ta ce tun farko an zaftare farashin ne saboda bukukuwan Kirsimati da sabuwar shekara, kuma bayan ƙarƙarewar wannan bukukuwa farashin zai dawo yadda ya ke a baya.

Matatar ta jaddada cewa za ta ci gaba da aiki tuƙuri wajen daidaita farashin man tare da tabbatar da wadatuwarsa a sassan ƙasar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp