Home Labarai Matatar man Ɗangote ta ƙara farashin man fetur da naira 100

Matatar man Ɗangote ta ƙara farashin man fetur da naira 100

Matatar Dangote

Matatar Man Ɗangote ta sanar da ƙarin farashin naira 100 kan kowacce litar man fetur guda inda a yanzu ta sanar da cewa za ta koma sayar da man akan farashinj naira 799.

Tun daga ranar 12 ga watan Disamban bara matatar ke sayar da kowacce litar man guda kan farashin naira 699 sai dai a wata sanarwa da ta fitar a jiya Litinin, ta ce farashin ya sauya nan ta ke.

Sanarwar matatar ta ce gidajen manta na MRS za su koma sayar da kowacce lita guda a farashin naira 839 daga naira 739 da suke sayarwa a baya.

Sanarwar ta Ɗangote ta ce tun farko an zaftare farashin ne saboda bukukuwan Kirsimati da sabuwar shekara, kuma bayan ƙarƙarewar wannan bukukuwa farashin zai dawo yadda ya ke a baya.

Matatar ta jaddada cewa za ta ci gaba da aiki tuƙuri wajen daidaita farashin man tare da tabbatar da wadatuwarsa a sassan ƙasar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp