Home Labarai Tallafi: Buhari ya Bada Umarnin Raba Kayan Abinci Ga ‘Yan Nijeriya

Tallafi: Buhari ya Bada Umarnin Raba Kayan Abinci Ga ‘Yan Nijeriya

President-Muhammadu-Buhari

 

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya ba da umarnin cewa a gaggauta sakin tan 40,000 na kayan Abinci daga asusun ajiyar hatsi na Gwamnatin Tarayya, domin taimakawa marasa karfi a yayin gudanar da bukukuwan Easter da sallah.

Ministan Noma da Raya Karkara Muhammed Mahmoud ne ya bayyana hakan a yayin da yake ganawa da manema labarai na Fadar Shugaban Kasa bayan wata ganawar sirri da Shugaba Muhammadu Buhari a fadar sa dake birnin tarayya Abuja a ranar Talata.

Mahmood, yace Shugaba Buhari ya bashi umarnin raba kayayyakin ga Al’ummar Nijeriya, ya kuma bayyana cewa yana fatan rabon kayan abincin zai ragewa Al’umma radadin hauhawar farashin kayan masarufi.

Ya kara da cewa, ton dubu 12 daga cikin dubu 40 da aka amince dasu za’a baiwa ma’aikatar kula da jin kai da bala’oi da ci gaban jama’a ta tarayya domin rabawa ‘yan gudun hijira a fadin kasar nan.

Economic Confidential ta rawaito ministan na cewa za’a yi amfani da tsarin da aka bi a lokacin kullen Corona (covid-19) a shekarar 2020, wajen raba ton dubu 70 na kayan abinci a wasu jihohin ciki har da birnin tarayya Abuja.

“Idan dai zaku iya tunawa, lokacin kullen corona a kasar nan shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bada umarnin fidda hatsi domin rabawa masu karamin karfi a Nijeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp