Home Labarai Tallafi: Buhari ya Bada Umarnin Raba Kayan Abinci Ga ‘Yan Nijeriya

Tallafi: Buhari ya Bada Umarnin Raba Kayan Abinci Ga ‘Yan Nijeriya

President-Muhammadu-Buhari

 

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya ba da umarnin cewa a gaggauta sakin tan 40,000 na kayan Abinci daga asusun ajiyar hatsi na Gwamnatin Tarayya, domin taimakawa marasa karfi a yayin gudanar da bukukuwan Easter da sallah.

Ministan Noma da Raya Karkara Muhammed Mahmoud ne ya bayyana hakan a yayin da yake ganawa da manema labarai na Fadar Shugaban Kasa bayan wata ganawar sirri da Shugaba Muhammadu Buhari a fadar sa dake birnin tarayya Abuja a ranar Talata.

Mahmood, yace Shugaba Buhari ya bashi umarnin raba kayayyakin ga Al’ummar Nijeriya, ya kuma bayyana cewa yana fatan rabon kayan abincin zai ragewa Al’umma radadin hauhawar farashin kayan masarufi.

Ya kara da cewa, ton dubu 12 daga cikin dubu 40 da aka amince dasu za’a baiwa ma’aikatar kula da jin kai da bala’oi da ci gaban jama’a ta tarayya domin rabawa ‘yan gudun hijira a fadin kasar nan.

Economic Confidential ta rawaito ministan na cewa za’a yi amfani da tsarin da aka bi a lokacin kullen Corona (covid-19) a shekarar 2020, wajen raba ton dubu 70 na kayan abinci a wasu jihohin ciki har da birnin tarayya Abuja.

“Idan dai zaku iya tunawa, lokacin kullen corona a kasar nan shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bada umarnin fidda hatsi domin rabawa masu karamin karfi a Nijeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp