Home SIYASA Yanzu – Yanzu: Dattawan Arewa Sun Bukaci Buhari yayi Murabus

Yanzu – Yanzu: Dattawan Arewa Sun Bukaci Buhari yayi Murabus

Kungiyar Dattawan Arewancin Nijeriya ta bukaci Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya sauka daga shugabancin Kasar, sakamakon kashe-kashen rayuka dake faruwa a fadin kasar, musamman Arewaci.

Daraktan Yada Labarai da  Shawarwari na Kungiyar Dr. Hakeem Baba-Ahmed ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.

“Gwamnatin Shugaban Muhammadu Buhari bata da abinda zata ce mana a fannin tsaro, sakamakon kalubalen da muke fuskata. baza mu iya cigaba da zama karkashin umarnin masu kashe mutane, Garkuwa, Fyade da dukkannin kungiyoyin dake tauye hikkin mu na rayuwa, kuma su kasance cikin kwanciyar hankali da nutsuwa ba, duk da irin wadannan muggan ayyukan da suke aikatawa.

“Kundin Tsarin Mulkin mu ya tanadi cewa Shugabanni suyi Murabus bisa radin kansu, idan aka kalubalance su da wasu dalilai, ko kuma suka gaza a harkokin shugabanci.

Sanarwar ta ce,”yanzu lokaci ya yi da Shugaba Buhari zai yi la’aka da wannan zabi. Tun da shugabancinsa ya gaza iya samar da inganataccem tsaro ga ‘yan Nijeriya. Kungiyar mu na sane da wannan shawara, kuma ba za mu ci gaba da rayuwa a cikin  wannan yanayi ba har sai shekarar 2023 lokacin da wa’adin shugaban Buharin zai kare.

Kungiyar ta kuma ce ta bayar da wannan shawara ne la’akari da nauyin daya rataya a wuyansa, sannan kuma ta bukaci wadanda yake jin maganar su dasu bashi shawarar ya yi murabus.

Ta cikin sanarwa kungiyar ta bayyana bakin cikin ta kan abinda ta kira kashe-kashen gami da cin zarafin Al’umma ya zama tamkar Ruwan dare, yanzu yin Balaguto ga ‘Yan Nijeriya ya zama hadari, kuma idan mutum ya zauna a gida ma bai tsira ba.

Ta cikin sanarwar kungiyar ta bukaci dukkannin masu zawarcin kujerar shugaban kasa a kakar zaben 2023, da suyi karatun ta Nutsa, su lura da kalubalen shugabanci dake gaban su da idon basira.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp