Home SIYASA Yanzu – Yanzu: Dattawan Arewa Sun Bukaci Buhari yayi Murabus

Yanzu – Yanzu: Dattawan Arewa Sun Bukaci Buhari yayi Murabus

Kungiyar Dattawan Arewancin Nijeriya ta bukaci Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya sauka daga shugabancin Kasar, sakamakon kashe-kashen rayuka dake faruwa a fadin kasar, musamman Arewaci.

Daraktan Yada Labarai da  Shawarwari na Kungiyar Dr. Hakeem Baba-Ahmed ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.

“Gwamnatin Shugaban Muhammadu Buhari bata da abinda zata ce mana a fannin tsaro, sakamakon kalubalen da muke fuskata. baza mu iya cigaba da zama karkashin umarnin masu kashe mutane, Garkuwa, Fyade da dukkannin kungiyoyin dake tauye hikkin mu na rayuwa, kuma su kasance cikin kwanciyar hankali da nutsuwa ba, duk da irin wadannan muggan ayyukan da suke aikatawa.

“Kundin Tsarin Mulkin mu ya tanadi cewa Shugabanni suyi Murabus bisa radin kansu, idan aka kalubalance su da wasu dalilai, ko kuma suka gaza a harkokin shugabanci.

Sanarwar ta ce,”yanzu lokaci ya yi da Shugaba Buhari zai yi la’aka da wannan zabi. Tun da shugabancinsa ya gaza iya samar da inganataccem tsaro ga ‘yan Nijeriya. Kungiyar mu na sane da wannan shawara, kuma ba za mu ci gaba da rayuwa a cikin  wannan yanayi ba har sai shekarar 2023 lokacin da wa’adin shugaban Buharin zai kare.

Kungiyar ta kuma ce ta bayar da wannan shawara ne la’akari da nauyin daya rataya a wuyansa, sannan kuma ta bukaci wadanda yake jin maganar su dasu bashi shawarar ya yi murabus.

Ta cikin sanarwa kungiyar ta bayyana bakin cikin ta kan abinda ta kira kashe-kashen gami da cin zarafin Al’umma ya zama tamkar Ruwan dare, yanzu yin Balaguto ga ‘Yan Nijeriya ya zama hadari, kuma idan mutum ya zauna a gida ma bai tsira ba.

Ta cikin sanarwar kungiyar ta bukaci dukkannin masu zawarcin kujerar shugaban kasa a kakar zaben 2023, da suyi karatun ta Nutsa, su lura da kalubalen shugabanci dake gaban su da idon basira.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp