Home Labarai Tsaro: Rundunar Sojin Najeriya sun gano Naira Miliyan 60 da za a...

Tsaro: Rundunar Sojin Najeriya sun gano Naira Miliyan 60 da za a kai wa ‘Yan Bindiga Kudin fansa

Rundunar Sojin Najeriya ta ce Dakarunta sun bankado Naira Miliyan 60 da ake kokarin kai wa ‘yan ta’adda kudin fansar karbo wasu daga cikin wadanda ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su.

Haka kuma, dakarun sun yi nasarar kubutar da wasu mutane da aka yi garkuwa da su da suka hadar da mata da kananan yara.

Dakarun, wadanda suka hada da sojin sama da na kasa, sun kai ga cin karfin ‘yan bindigar. Inda suka bankado tare da kwato muggan makamai da bindiga kirar AK47, da albarusai da sauransu.

Jaridar PRNigeria ta rawaito cewar, cikin wadanda ake zargin zasu kai kudin fansar  akwai jami’in tsaro na farin kaya wato DSS.

Wani jami’in liken asiri ya shaidawa PRNigeria cewa dakarun sojin saman bataliya ta 271 a Birnin Gwarri, da Dakarun FOB na  Gwaska, sun kubutar da dimbin mutanen da aka yi garkuwa da su a yayin atisayen na hadin gwuiwa.

Jami’in ya ce: “An kwato zunzurutun kudi kimanin Naira Miliyan 60, Man Fetur da kuma muggan makamai, a yayin gudanar da aikin.

“Sauran kayayyakin da sojojin suka kwato daga hannun wadanda ake zargin sun hadar da Motoci, Bindigu kirar AK-47 Alburusai iri-iri da kuma wayoyin hannun.

“Za kuma a mika batun jami’an tsaron da suka hada da na DSS da ake zargi da kai kudin fansar ga ma’aikatar tsaron Najeriya, domin gudanar da bincike.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp