Home Labarai An ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin Nijar

An ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin Nijar

A daren jiya ne aka ji ƙarar harbe-harbe da fashe-fashe a filin jirgin sama na ƙasa da ƙasa na Diori Hamari da ke babban birnin Niamey na Jamhuriyar Nijar.

Kafar LSI Africa ce ta ruwaito labarin daga wasu shaidun gani da ido, inda suka ce an fara jin ƙarar ne da misalin ƙarfe 12 na dare, sannan ya ɗan ɗauki lokaci ana yi.

Wasu faye-fayen bidiyo da suka karaɗe kafofin sada zumunta a ƙasar sun nuna yadda haske ya yi sama daga daidai yankin da ake jin harbe-harben.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton dai hukumomi a ƙasar ba su ce komai ba kan aukuwar lamarin, musamman kan musabbin harbe-harbe da fashe-fashen ko asarar da aka yi, da kuma ko an rasa rai.

Sai dai akwai rahotannin da ba a tabbatar ba da ke zargin wataƙila mayaƙa masu iƙirarin jihadi ne suka yi yunƙurin kai hari a filin jirgin.

Sai dai wasu na zargin ganin yanayin ƙarar wataƙila akwai yiwuwar wata matsala ce ta cikin gida da ba za ta rasa nasaba da boren sojoji ba, kamar yadda rahoton ya ƙara.

Nijar dai na fama da matsalolin rashin tsaro a cikin ƴan shekarun nan duk da cewa tana ƙarƙashin mulkin Janar Abdourahmane Tchiani, wanda ya karɓi mulki bayan juyin mulkin watan Yulin 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp