Home Labarai An ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin Nijar

An ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin Nijar

A daren jiya ne aka ji ƙarar harbe-harbe da fashe-fashe a filin jirgin sama na ƙasa da ƙasa na Diori Hamari da ke babban birnin Niamey na Jamhuriyar Nijar.

Kafar LSI Africa ce ta ruwaito labarin daga wasu shaidun gani da ido, inda suka ce an fara jin ƙarar ne da misalin ƙarfe 12 na dare, sannan ya ɗan ɗauki lokaci ana yi.

Wasu faye-fayen bidiyo da suka karaɗe kafofin sada zumunta a ƙasar sun nuna yadda haske ya yi sama daga daidai yankin da ake jin harbe-harben.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton dai hukumomi a ƙasar ba su ce komai ba kan aukuwar lamarin, musamman kan musabbin harbe-harbe da fashe-fashen ko asarar da aka yi, da kuma ko an rasa rai.

Sai dai akwai rahotannin da ba a tabbatar ba da ke zargin wataƙila mayaƙa masu iƙirarin jihadi ne suka yi yunƙurin kai hari a filin jirgin.

Sai dai wasu na zargin ganin yanayin ƙarar wataƙila akwai yiwuwar wata matsala ce ta cikin gida da ba za ta rasa nasaba da boren sojoji ba, kamar yadda rahoton ya ƙara.

Nijar dai na fama da matsalolin rashin tsaro a cikin ƴan shekarun nan duk da cewa tana ƙarƙashin mulkin Janar Abdourahmane Tchiani, wanda ya karɓi mulki bayan juyin mulkin watan Yulin 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp