Kalaman Nuna Gazawar Ministan Ilimin Nijeriya sun bar baya da Kura

Kalaman ministan ilimin Nijeriya Adamu Adamu na cigaba da yamutsa hazo a kasar, inda wa suke ganin cewa kamata yayi ace ya ajje mukamin tun da fari daya fahimci gazawar tasa.

Tun da fari dai yayin wani taron majalisar iimi ta kasa karo na 66 ranar alhamis a birnin tarayya abuja an jiwo ministan na bayyana cewa ya gaza a matsayin sa na ministan ilimi a kasar.

Wannan kamalami na ministan na zuwa ne bayan gazawa da yayi wajen warware kalubalen da dama daya kamata ya warware kasancewar sa minister mafi dadea akan harkokin ilimi a kasar.

Sai dai yayin jawabin ya zargi ma’aikatun ilimi na jihohi da kara ingiza wasu abubuwa da suka taimaka wajen gazawar ta sa matsayin ministan ilimi.

Yace kama daga kan karin yawan yaran da basa zuwa makaranta da aka samu a kasar har zuwa ga kalubalen kungiyar malaman jami’oin kasar ta ASUU da sauran da sauran matsalolin dake kara tabarbara harkokin ilimi manyan makarantu, wanda ya gaza samar da mafitar shawo kan matsalolin.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 45 minutes 32 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 26 minutes 57 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com