Home Labarai UNICEF: Yara Sama da Dubu 14 na Cikin Hadarin Kamuwa da...

UNICEF: Yara Sama da Dubu 14 na Cikin Hadarin Kamuwa da Cutar Yunwa a Nijeriya

Asusun tallafawa kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya yi gargadin cewa kananan yara miliyan 14 da dubu 700 a Najeriya galibinsu ‘yan kasa da shekaru 5 da haihuwa na cikin hadarin kamuwa da cutar Tamowa wadda karancin abinci me gina jiki ke haddasawa.

Asusu na UNICEF ya bayyana cewa idan har ba a dauki matakan da suka kamata ba, a cikin shekarar dake shirinkarewa, yara miliyan 13 za su fuskanci cutar tamowa yayin da wasu miliyan 1 da dubu 700 kuma za su fuskanci matsananciyar cutar ta Tamowa galibi a yankin arewacin Najeriyar

Asusun na UNICEF ya ce abin takaici ne yadda alkaluma ke nuna mutuwar kananan yara 100 ‘yan kasa da shekaru 5 da haihuwa duk bayan sa’a daya a Najeriya, yayin da wasu yaran na daban miliyan 12 ke cikin halin matsanancin rashin abinci.

Shugabar sashen abinci mai gina jiki ta UNICEF a Najeriya Nemat Hajeebhoy, ta ce yara a Najeriya na halin tsananin bukatar abinci mai gina jiki lura da yanayin da kasar ke ciki na tabarbarewar tattalin arzki da ya sanya iyalai gaza samun isasshen abinci.

A cewar jami’ar matsaloli masu alaka da ambaliyar ruwa da ta lalata tarin amfanin gona a sassan Najeriya na shirin sake tsananta karuwar yaran da ke fama da wannan cuta ta rashin isasshen abinci mai gina jiki wato cutar yunwa ko kuma Tamowa.

Nemat Hejeebhoy ta ce za a fuskanci karuwar yara masu fama da matsalar cutar ta Tamowa a 2023 saboda karancin abinci da Najeriya za ta fuskanta mai alaka da sauyin yanayi.

UNICEF ta ce idan har gwamnatoci da sauran wadanda abin ya shafa basu dauki matakan da suka kamata ba, rayuwar kananan yaran masu fama da yunwa na cikin hadarin gaske, kari kan miliyoyin yaran da yanzu haka ke fama da cutar ta Tamowa.

UNICEF

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp