Home Labarai Ganduje na Shirin Daukar Matakin Shari’a kan Jaridar Sahara Reporters

Ganduje na Shirin Daukar Matakin Shari’a kan Jaridar Sahara Reporters

Gwamnatin jihar Kano ta yi Allah-wadai da kakkausar murya da ikirarin wata kafar yada labarai ta yanar gizo ta yi na cewa, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na daya daga cikin gwamnoni uku da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arziki Ta’annati (EFCC) ta bayyana da boye kudade a gidajensu.

A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Malam Muhammad Garba ya fitar ta nuna cewa, hukumar EFCC ba ta lissafa sunayen gwamnonin da take zargi ba, amma jaridar ta bayyana sunan gwamnoni akan karya.

Ya ce rahoton da kafar ta fitar, ba shi da tushe a labaran bincike, sai dai kawai hasashe na mawallafa ko kuma wani yunkuri na bata sunan gwamnan da gangan.

Malam Garba ya yi nuni da cewa, Gwamna Ganduje bai boye Biliyoyin Nairori a gida ba don biyan ma’aikatan gwamnatinsa albashi, sabida gujewar faduwar banki.

Kwamishinan ya kara da cewa jihar Kano na daya daga cikin jihohin tarayya da ke biyan albashin ma’aikata akan lokaci, a lokacin da da jaridar ta fitar da rahoton karya, an fara ba wasu Ma’aikatan jihar albashin watan Oktoba.

Don haka ya yi kira ga jaridar da ta janye labarin tare da neman gafarar gwamnatin ba tare da bata lokaci ba, gwamnatin jihar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen daukar matakin shari’a.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp