Home Labarai Ganduje na Shirin Daukar Matakin Shari’a kan Jaridar Sahara Reporters

Ganduje na Shirin Daukar Matakin Shari’a kan Jaridar Sahara Reporters

Gwamnatin jihar Kano ta yi Allah-wadai da kakkausar murya da ikirarin wata kafar yada labarai ta yanar gizo ta yi na cewa, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na daya daga cikin gwamnoni uku da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arziki Ta’annati (EFCC) ta bayyana da boye kudade a gidajensu.

A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Malam Muhammad Garba ya fitar ta nuna cewa, hukumar EFCC ba ta lissafa sunayen gwamnonin da take zargi ba, amma jaridar ta bayyana sunan gwamnoni akan karya.

Ya ce rahoton da kafar ta fitar, ba shi da tushe a labaran bincike, sai dai kawai hasashe na mawallafa ko kuma wani yunkuri na bata sunan gwamnan da gangan.

Malam Garba ya yi nuni da cewa, Gwamna Ganduje bai boye Biliyoyin Nairori a gida ba don biyan ma’aikatan gwamnatinsa albashi, sabida gujewar faduwar banki.

Kwamishinan ya kara da cewa jihar Kano na daya daga cikin jihohin tarayya da ke biyan albashin ma’aikata akan lokaci, a lokacin da da jaridar ta fitar da rahoton karya, an fara ba wasu Ma’aikatan jihar albashin watan Oktoba.

Don haka ya yi kira ga jaridar da ta janye labarin tare da neman gafarar gwamnatin ba tare da bata lokaci ba, gwamnatin jihar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen daukar matakin shari’a.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp