Home Labarai Hukumar NDLEA ta Kama Masu Safarar Koken daga Kasashen Ketare zuwa Kasar

Hukumar NDLEA ta Kama Masu Safarar Koken daga Kasashen Ketare zuwa Kasar

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya NDLEA ta ce jami’anta sun kama wani ɗan Nijar da ‘yan Pakistan biyu bisa zargin safarar koken.

A sakon da hukumar ta wallafa a shafinta na Tuwita ta ce an kama ‘yan Pakistan din a filin jirgin sama na Legas da ke kudu maso yammacin Najeriya, yayin da aka kama ɗan Nijar ɗin a jihar Katsina da ke arewa maso yammacin ƙasar

Hukumar ta ce ta kama ‘yan Pakistan ɗin – masu suna Asif Muhammed mai shekara 45, da kuma Hussain Naveed, mai shekara 57 – da laifin safarar koken da nauyinta ya kai kilo 2,985.5kg, a yayin da suke shirin hawa jirgi zuwa birnin Lahore na Pakistan.

Sanarwar ta ci gaba da cewa mutanen na da takardun izinin zama a Najeriya, waɗanda take zargin cewa na bogi ne, kuma suna yawan zuwa Najeriya da nufin yin kasuwancin atamfofi.

Emergency Digest

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp