Home Labarai Hukumar NDLEA ta Kama Masu Safarar Koken daga Kasashen Ketare zuwa Kasar

Hukumar NDLEA ta Kama Masu Safarar Koken daga Kasashen Ketare zuwa Kasar

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya NDLEA ta ce jami’anta sun kama wani ɗan Nijar da ‘yan Pakistan biyu bisa zargin safarar koken.

A sakon da hukumar ta wallafa a shafinta na Tuwita ta ce an kama ‘yan Pakistan din a filin jirgin sama na Legas da ke kudu maso yammacin Najeriya, yayin da aka kama ɗan Nijar ɗin a jihar Katsina da ke arewa maso yammacin ƙasar

Hukumar ta ce ta kama ‘yan Pakistan ɗin – masu suna Asif Muhammed mai shekara 45, da kuma Hussain Naveed, mai shekara 57 – da laifin safarar koken da nauyinta ya kai kilo 2,985.5kg, a yayin da suke shirin hawa jirgi zuwa birnin Lahore na Pakistan.

Sanarwar ta ci gaba da cewa mutanen na da takardun izinin zama a Najeriya, waɗanda take zargin cewa na bogi ne, kuma suna yawan zuwa Najeriya da nufin yin kasuwancin atamfofi.

Emergency Digest

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp