Home DUNIYA Ana Zanga-Zanga A Ghana Saboda Tsadar Rayuwa

Ana Zanga-Zanga A Ghana Saboda Tsadar Rayuwa

Daruruwan ‘yan Ghana sun fantsama kan titunan birnin Accra, suna kira ga shugaban kasar, Nana Akufo-Addo da ya yi murabus sakamakon tsadar rayuwa da kuma gazawar gwamnatinsa wajen tunkarar matsalar tattalin ariki.

A makon da ya gabata ne shugaba Akufo-Addo ya roki ‘yan kasar da su amince da shirinsa na karbo bashi daga Asusun Bada Lamuni na Duniya IMF duk da cewa, wani lokaci a can baya, ya taba yi wa ‘yan kasar alkawarin cewa, ba za su ciyo basuka ba.

Yanzu haka dai matsalar tattalin arziki ta shafi kusan kowanne bangare na al’ummar kasar ta Ghana da suka hada da masu hali da talakawa.

Wasu daga cikin masu zanga-zangar da suka zanta da manema labarai sun ce, babu abin da suke son gani face shugaban kasar da wasu mukarrabansa su yi murabus saboda sun gaji da yadda kasar ke tafiya a cewarsu.

Ghana dai na neman rancen Dala biliyan 3 daga Asusun Bada Lamuni na Duniya IMF domin shawo kan matsalar hau-hawan farashi da kashi 37  da kuma magance zubewar darajar kudin kasar na Cedi.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp