Home DUNIYA Manoma Afrika da Asiya zasu Rabauta da Tallafin Dala biliyan 1.4

Manoma Afrika da Asiya zasu Rabauta da Tallafin Dala biliyan 1.4

An bukaci kasashe masu karfin mawadata da su biya diyar kudade ga takwarorin su matalauta, sakamakon yadda suka haddasa aukuwar musibu masu nasaba da sauyin yanayi a kasashen nasu.

Wanan na zuwa ne bayan bude taron sauyin yanayi na Majalisar Dinkin Duniya mai take COP27 dake gudana a kasar Masar.

Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya mai tada hankali ya ce, shekaru takwas da suka shude na baya-bayan nan, sun zama mafi samun dumamar yanayi a tarihi, inda aka samu tumbatsar tekuna, narkewar tsaunukan kankara , tsananin zafi da dai sauran ibtila’o’in da ke nuni da sauyin yanayi.

Sakatere Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guteress ya ce, a daidai lokacin da aka bude taron  na COP27, wannan doran duniyar da muke rayuwa a kai, na aikewa da mummunan sako.

A ‘yan watanni da ssuka gabata, ambaliyar ruwa ta yi barna sosai a kasashe irinsu Pakistan da Najeriya, sannan matsalar fari ta yi kamari a nahiyar Afrika da Amurka, yayin da kuma guguwa ta yi shara a yankin Caribbean, inda kuma aka samu wani irin zafi mai tsanani da ba a taba gani ba a nahiyoyi uku na duniya.

Taron na COP27 da ke gudana a wurin shakatawa na Sharm el-Sheikh da ke kasar Masar, na zuwa ne a daidai lokacin da ake gwabza yaki tsakanin Rasha da Ukraine, al’amarin da ya haddasa hau-hawan farashin kayyaki a sassan duniya.

Taron na bana zai fi mayar da hankali ne kan yadda za a tara kudaden tunkarar matsalar ta sauyin yanayi.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp