Home Labarai SERAP ta bukaci Tinubu ya binciki bashin dala biliyan 1.5 da jihohi...

SERAP ta bukaci Tinubu ya binciki bashin dala biliyan 1.5 da jihohi 36 suka karbo

Kungiyar  dake yaki da cin hanci da daidaito na harkokin gwamnati SERAP ta bukaci shugaban kasa Bola Tinubu ya binciki bashin dala biliyan 1.5 na bankin duniya da jihohi 36 suka karbo tare da babban birnin tarayya.

Kungiyar ta kuma bukaci Tinubu da ya binciki zargin karkatar da lamunin China na $3.121bn da gwamnatin tarayya ta tarba.

SERAP ta roki Shugaban kasa da ya umarci Babban antoni janar na kasa kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi, da hukumomin da suka dace da yaki da cin hanci da rashawa da su gaggauta yin bincike sosai kan yadda aka kashe rancen, ta yadda za a rage “talauci da inganta rayuwar al’umma a fadin jihohin kasarnan.”

Hakan na kunshe ne a wata budaddiyar wasika mai kwanan watan Agusta 10, 2024, mai dauke da sa hannun Mataimakin Daraktan kungiyar, Kolawole Oluwadare.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp