Home Labarai Fadar shugaban Kasa ta magantu kan zargin da Kwankwaso ya yiwa Tinubu

Fadar shugaban Kasa ta magantu kan zargin da Kwankwaso ya yiwa Tinubu

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta zargin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso cewa gwamnatin Bola Tinubu ta watsar da yankin Arewa, tana mai cewa arewacin Najeriya na samun gagarumin kulawa a ayyukan ci gaba.
Kwankwaso, a wani taron tattaunawa kan gyaran kundin tsarin mulki da aka gudanar a Kano, ya soki gwamnatin Tinubu da karkatar da albarkatun ƙasa zuwa kudu, yana mai cewa hakan na ƙara jefa Arewa cikin fatara da rashin tsaro. Ya kuma koka da halin da titunan tarayya ke ciki a yankin, inda ya bada misalin wata tafiyarsa daga Abuja zuwa Kano da ya kira da “azaba” sakamakon lalacewar hanya.
Sai dai da yake mayar da martani, mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, Sunday Dare, ya ce kalaman Kwankwaso sun saba wa gaskiya, domin gwamnatin Tinubu na aiwatar da manyan ayyuka a Arewa da suka shafi hanyoyi, noma, lafiya da makamashi.
Ya lissafa muhimman ayyuka kamar titin Abuja–Kaduna–Kano, bututun iskar gas na Ajaokuta–Kaduna–Kano, shirin noma a jihohi tara, da aikin Kolmani a Bauchi da Gombe. Ya kuma ce an farfaɗo da cibiyoyin lafiya 1,000 a Arewa tare da bunƙasa wasu asibitoci manya.
Dare ya ƙara da cewa duk waɗannan nasarori an cimma su ne a cikin shekaru biyu kacal da Shugaba Tinubu ya hau mulki, yana mai cewa Arewa na da muhimmiyar matsayi a tsarin ci gaban gwamnatin.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp