Home Taska Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar Benue

Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar Benue

'Yan Ta'adda

Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar Benue

 

Aƙalla mutum 10 aka kashe da sanyin safiyar Laraba bayan wasu mahara ɗauke da makamai sun kai hari ƙauyen Saai da ke gundumar Mbajir a ƙaramar hukumar Katsina-Ala ta jihar Benue.

Mazauna yankin sun ce maharan sun kutsa cikin ƙauyen da tsakar dare, inda suka riƙa harbe-harbe ba tare da ƙaƙƙautawa ba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito wani mazaunin yankin na cewa wasu daga cikin mutanen sun jikkata sakamakon harbin bindiga, yayin da aka kashe wasu ciki har da Mchiaga Akaa Agbondo, wanda ya ce “an sassara shi da adda har ba a gane fuskarsa”.

Ya ƙara da cewa ana ci gaba da kula da wasu da suka jikkata a asibiti.

Shugaban ƙaramar hukumar Katsina-Ala, Justine Shaku, ya tabbatar da faruwar harin, amma ya ce har yanzu ba a tantance adadin mutanen da suka mutu ba, amma ya je yankin domin duba halin da ake ciki.

Gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia, ya yi Allah wadai da harin, inda ya yi zargin cewa maharan ƴan ta’adda ne da ke fakewa da sunan makiyaya, domi kawo cikas ga ayyukan noma da samar da abinci a jihar.

Gwamnan ya umarci jami’an tsaro su tura ƙarin dakaru zuwa yankin Saai da sauran ƙauyukan da ke makwabtaka da yankin domin farautar waɗanda suka kai harin, tare da ƙara tsaurara matakan tsaro ga manoma.

Rundunar ƴansanda ba ta fitar da wata saarwa game da harin ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin Najeriya
X whatsapp