Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar Benue
Aƙalla mutum 10 aka kashe da sanyin safiyar Laraba bayan wasu mahara ɗauke da makamai sun kai hari ƙauyen Saai da ke gundumar Mbajir a ƙaramar hukumar Katsina-Ala ta jihar Benue.
Mazauna yankin sun ce maharan sun kutsa cikin ƙauyen da tsakar dare, inda suka riƙa harbe-harbe ba tare da ƙaƙƙautawa ba.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito wani mazaunin yankin na cewa wasu daga cikin mutanen sun jikkata sakamakon harbin bindiga, yayin da aka kashe wasu ciki har da Mchiaga Akaa Agbondo, wanda ya ce “an sassara shi da adda har ba a gane fuskarsa”.
Read Also:
Ya ƙara da cewa ana ci gaba da kula da wasu da suka jikkata a asibiti.
Shugaban ƙaramar hukumar Katsina-Ala, Justine Shaku, ya tabbatar da faruwar harin, amma ya ce har yanzu ba a tantance adadin mutanen da suka mutu ba, amma ya je yankin domin duba halin da ake ciki.
Gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia, ya yi Allah wadai da harin, inda ya yi zargin cewa maharan ƴan ta’adda ne da ke fakewa da sunan makiyaya, domi kawo cikas ga ayyukan noma da samar da abinci a jihar.
Gwamnan ya umarci jami’an tsaro su tura ƙarin dakaru zuwa yankin Saai da sauran ƙauyukan da ke makwabtaka da yankin domin farautar waɗanda suka kai harin, tare da ƙara tsaurara matakan tsaro ga manoma.
Rundunar ƴansanda ba ta fitar da wata saarwa game da harin ba.










