Home Taska An Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban...

An Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos

An Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta gurfanar da mutum 24 a gaban kotun majistare bisa zarginsu da hannu a kisan wata matar aure da wasu fusatattun mutane suka yi a Maraban Jos.

Ana tuhumar waɗanda ake zargin da laifukan bayar da gudummuwa wajen aikata laifi, tayar da hankalin jama’a, lalata dukiyoyi, lalata kadarorin gwamnati da na ‘yan sanda, da kuma kisan kai.

Wata sanarwa da kakakin rundunar ta jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya fitar ta ce an gurfanar da su ne bayan binciken da ‘yan sanda suka gudanar kan lamarin da ya faru a ranar 21 ga Yunin 2026, lokacin da aka kashe matar “bayan mutanen sun ƙwace ta daga hannun ‘yan sanda.”

An ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 21 ga Yulin 2026, inda kotun ta bayar da umarnin a tsare dukkan waɗanda ake zargin a gidan yari har sai an kammala shari’ar.

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ƙara da cewa har yanzu ana ci gaba da binciken fiye da mutum 100 da ake zargin su da hannu a lamarin, tare da alƙawarin gurfanar da duk wanda bincike ya nuna yana da laifi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban JosMatsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna An Zargi Kwankwaso da Sayen Fom ɗin Takara na Kujeru 69 a Jam'iyyar PRPƘasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar SokotoMasu Iƙirarin Jihadi Sun Hallaka Manoma 11 a Jihar Borno 'Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami'an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum 1 a Jihar KebbiTaron NUJ: Lokacin Da Manyan Jami’an Tsaro Suka Guji Yan Jarida Daga Yushau A. ShuaibSamar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46Ta'addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke AbujaAn Ceto Matar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaHauhawar Farashin Kayan Masarufi a Najeriya ya ƙaru Zuwa Kashi 15.93Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar Katsina
X whatsapp