An Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta gurfanar da mutum 24 a gaban kotun majistare bisa zarginsu da hannu a kisan wata matar aure da wasu fusatattun mutane suka yi a Maraban Jos.
Ana tuhumar waɗanda ake zargin da laifukan bayar da gudummuwa wajen aikata laifi, tayar da hankalin jama’a, lalata dukiyoyi, lalata kadarorin gwamnati da na ‘yan sanda, da kuma kisan kai.
Read Also:
Wata sanarwa da kakakin rundunar ta jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya fitar ta ce an gurfanar da su ne bayan binciken da ‘yan sanda suka gudanar kan lamarin da ya faru a ranar 21 ga Yunin 2026, lokacin da aka kashe matar “bayan mutanen sun ƙwace ta daga hannun ‘yan sanda.”
An ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 21 ga Yulin 2026, inda kotun ta bayar da umarnin a tsare dukkan waɗanda ake zargin a gidan yari har sai an kammala shari’ar.
Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ƙara da cewa har yanzu ana ci gaba da binciken fiye da mutum 100 da ake zargin su da hannu a lamarin, tare da alƙawarin gurfanar da duk wanda bincike ya nuna yana da laifi.










