Home Taska Matsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna 

Matsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna 

Matsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna 

 

Harin ya sake jefa al’ummomin yankin cikin jimami da fargaba, duk da ƙoƙarin da ake yi na dawo da zaman lafiya.

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe manoma shida yayin da suke aiki a gonakinsu a yankin Kujijiro da ke Gundumar Kuyello ta Ƙaramar Hukumar Birnin Gwari a Jihar Kaduna.

Ƙungiyar Birnin Gwari Emirate Progressives Union (BEPU) ta tabbatar da harin, tana mai bayyana lamarin a matsayin abin takaici da tayar da hankali.

A cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar, Dakta Isa Muhammad, ya fitar, ya ce harin ya sake jefa al’ummomin yankin cikin jimami da fargaba, duk da ƙoƙarin da ake yi na dawo da zaman lafiya.

Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa ci gaba da kai hare-hare kan manoma na iya hana mutane komawa gonakinsu a wannan kakar noma, lamarin da ka iya shafar samar da abinci da kuma ƙara tsadar rayuwa.

BEPU ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Kaduna da su ƙara kaimi wajen magance matsalar tsaro a Birnin Gwari da maƙwabtanta.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, gwamnatin jihar da rundunar ’yan sanda ba su fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INECJam'iyyar NDC ta Buƙaci Sanata Hanga da Gaya da su Sake Tunani Kan Sauya SheƙaYan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi MataimakinsaJami'an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto 
X whatsapp