Home Taska Matsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna 

Matsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna 

Matsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna 

 

Harin ya sake jefa al’ummomin yankin cikin jimami da fargaba, duk da ƙoƙarin da ake yi na dawo da zaman lafiya.

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe manoma shida yayin da suke aiki a gonakinsu a yankin Kujijiro da ke Gundumar Kuyello ta Ƙaramar Hukumar Birnin Gwari a Jihar Kaduna.

Ƙungiyar Birnin Gwari Emirate Progressives Union (BEPU) ta tabbatar da harin, tana mai bayyana lamarin a matsayin abin takaici da tayar da hankali.

A cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar, Dakta Isa Muhammad, ya fitar, ya ce harin ya sake jefa al’ummomin yankin cikin jimami da fargaba, duk da ƙoƙarin da ake yi na dawo da zaman lafiya.

Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa ci gaba da kai hare-hare kan manoma na iya hana mutane komawa gonakinsu a wannan kakar noma, lamarin da ka iya shafar samar da abinci da kuma ƙara tsadar rayuwa.

BEPU ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Kaduna da su ƙara kaimi wajen magance matsalar tsaro a Birnin Gwari da maƙwabtanta.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, gwamnatin jihar da rundunar ’yan sanda ba su fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga Legas
X whatsapp