Home Taska Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP – Rundunar Sojin Najeriya

Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP – Rundunar Sojin Najeriya

Rundunar Soji

Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP – Rundunar Sojin Najeriya

 

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation Hadin Kai a yankin Arewa maso Gabas ta ceto mutum 47, yawancinsu mata da ƙananan yara, da mayaƙan ISWAP suka tsare a yankin Kangarwa da ke ƙaramar hukumar Kukawa a jihar Borno.

A cikin sanarwar da rundunar ta fitar, ta bayyana cewa an samu nasarar ceto mutanen ne a ranar 20 ga watan Yuni 2026, bayan wani gagarumin samame da sojojinta suka kai wanda ya tilasta ‘yan ta’addar tserewa suka bar waɗanda suka sace.

Ya ce hare-haren kasa da na sama da dakarun suka kai wa sansanonin ISWAP a yankin Tafkin Chadi ne ya sa ‘yan ta’addar suka rikice suka bar wuraren da suke, lamarin da ya bai wa wadanda aka tsare damar tsira bayan dogon lokaci a hannunsu.

A yanzu haka, an kai waɗanda aka ceto wuraren tsaro inda ake basu kulawar lafiya da taimakon jin kai, yayin da rundunar ta sake jaddada ƙudurinta na ci gaba da kawo ƙarshen ayyukan ta’addanci da dawo da zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Meyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu MohammedJami'an Tsaro Sun Kai Farmaki Sansanin IPOB/ESN, Sun Kawar da 'Yan Ta'adda 6 a AnambraOperation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Lalata Motocin Yaƙi Guda Biyu na ISWAP, Sannan Ya Kawar da Ƴan Ta'adda da Dama a BornoMai fafutuka Mahdi Shehu ya yi Gargadin Cewa Kudirin Dokar NGO Zai iya Shafar Masallatai, Coci, da Ƙungiyoyin ɗalibaiRikicin Karkashin Mulkin APC a Katsina: ADC na Radda da CSO Har Yanzu Suna Tsare a Hannun Masu ba Tinubu Shawara, MasariAnambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron Hanya
X whatsapp