Sanatoci za su Fara Duba ƙudirin Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba – Akpabio
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya aika wa Majalisar Dattawa ƙudirin dokar gyaran kundin tsarin mulki da ke neman kafa ƴan sandan jihohi.
Read Also:
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ne ya sanar da hakan a zaman majalisar na ranar Talata, inda ya ce sanatocin za su fara duba ƙudirin a ranar Laraba.
Akpabio ya kuma bayyana cewa su ma gwamnatocin jihohi su yi nazarin ƙudirin.
Ƙudirin dokar na neman a yi gyare-gyare ga wasu sassan kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 domin samar da tsarin doka da zai ba da damar kafa rundunar ƴan sandan jihohi a faɗin ƙasar.










