Mabiya Addinai Biyu a Najeriya Sun Sanya
Hannu Kan Sabuwar Yarjejeniya
Shugabannin addinin Musulunci da Kiristoci fiye da 50 ne suka rattaba hannu kan wata yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin mabiya addinan biyu a Najeriya,
An ƙaddamar da wata sabuwar ƙungiya da za ta mayar da hankali wajen inganta fahimtar juna da zaman lafiya tsakanin addinai, a taron da ƙungiyar Musulmi ta Duniya da ke da hedikwata a Saudiyya ta shirya a Abuja.
Read Also:
Yarjejeniyar ta zo ne watanni bayan da Shugaban Amurka Donald Trump ya zargi Najeriya da gaza kare Kiristoci daga hare-haren ƙungiyoyin masu ikirarin jihadi, tare da yin barazanar daukar matakin soji kan ƙasar.
Sai dai ba a yi magana kan kalaman Trump ba a taron da aka sanya hannu kan yarjejeniyar.
Sakatare Janar na ƙungiyar Musulmi ta Duniya, Mohammad Al-Issa, yana cewa dukkanin mabiya addinan biyu na maraba da wannan tsari da ya ce ya “buɗe sabon shafi”.
Shugabannin Musulmi da Kiristocin da suka halarci taron sun ce yarjejeniyar za ta iya taimakawa wajen rage kalaman ƙiyayya da rarrabuwar kawuna.
Mataimakin shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu wajen bikin, ya ce gwamnati ta kuduri aniyar ganin Najeriya ta ci gaba da kasancewa dunƙulalliyar ƙasa duk da bambance-bambancen da ke tsakaninta.











