Home Taska Hukumar NITDA ta Raba Kayan Aiki da Jari ga Matasa 140 Wadanda...

Hukumar NITDA ta Raba Kayan Aiki da Jari ga Matasa 140 Wadanda ta ba wa Horo Kan Gyaran Waya a Jihar Jigawa

Defence Minister Mansur Dan Ali Receives Souveniur from Italian Defence Minister Sen Roberta Pinnoti
Defence Minister Mansur Dan Ali Receives Souveniur from Italian Defence Minister Sen Roberta Pinnoti

Hukumar NITDA ta Raba Kayan Aiki da Jari ga Matasa 140 Wadanda ta ba wa Horo Kan Gyaran Waya a Jihar Jigawa

Hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), ƙarƙashin jagorancin Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), ta yaye matasa jimillar mutum (140) a Jihar Jigawa waɗanda ta ba wa horo kan sana’ar gyaran wayar salula a zamance gami da sauran harkokin fasaha, kana kuma ta raba musu jari haɗi da kayan aikin gudanar sana’ar domin dogaro da kai.

Horon na tsawon yini huɗu wanda aka gudanar da shi a ranar 31 ga watan Janairu, zuwa 4 ga watan Fabarairu, 2022 a cibiyoyi gudan biyu da aka ware a cikin garuruwan Dutse da Haɗejia, kowacce cibiya ta ɗauki jimilla mutane saba’in.

Kayan aikin sun haɗa da manyan wayoyi na hannu (Tablet), da sufanun sincewa da ɗaure waya, gami da kuɗin sufuri da sauransu. An kuma ilimantar da matasan salo da dabarun warware natsalolin wayar hannu a zamance.

Ko da a can baya, hukumar ta (NITDA) bisa kulawar ma’aikatar sadarwa da tattalin arziƙin fasahar zamani, ƙarƙashin jagorancin Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), ta ƙaddamar da irin wannan shiri a wasu daga cikin Jihohin ƙasar nan kamar Jihar Yobe. Manufar shirin ita ce fatan ganin matasa sun samu abin yi tattalin arziƙin ƙasa ya bunƙasa.

Litinin, 14 ga watan Fabarairu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp