‘Yan Sandan Najeriya Sun Kama Kasurgumin Mai Garkuwa da Mutane a Hanyar Abuja-Kaduna

‘Yan Sandan Najeriya Sun Kama Kasurgumin Mai Garkuwa da Mutane a Hanyar Abuja-Kaduna

Yan sanda a Najeriya sun ce sun kama wani da ake zargin kasurgumin mai garkuwa da mutane ne tare da wasu mutum 29 na daban,

‘Yan sandan sun ce mutane suna da hannu a yawancin garkuwar da ake yi da mutane da fashi da makami wadanda suka fi mayar da hankali a kan hanyar Abuja-Kaduna har da ma cikin Kaduna.

Mutumin mai shekara 36 ya amsa cewa shi yake jagorantar kungiyar, cikin wata sanarwa da ‘yan sanda suka fitar a yammacin Alhamis.

Hanyar Abuja-Kaduna na daya daga cikin hanyoyi masu matukar hadari a Najeriya yayin da masu garkuwa da mutane ke yi wa matafiya kwantan bauna a hanyar.

Sau da yawa ke kama harbin kan mai uwa da wabi domin tursasa musu tsayawa a hanya.

An kashe matafiya da yawa a hatsaniya wadanda kuma suka tsira sai a yi garkuwa da su kuma ana sakinsu ne bayan sun biya kudaden fansa.

Wannan dalili ya tilastawa mutane da dama daina bin hanyar suka koma jirgin kasa – wanda suke ganin hakan a matsayin wani tudun mun tsira daga bin hanyar.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 14 hours 33 minutes 14 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 16 hours 14 minutes 39 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here