Home Taska ‘Yan Kunar Bakin Wake Sun Kashe ‘Yar Majalisar Kasar Somaliya

‘Yan Kunar Bakin Wake Sun Kashe ‘Yar Majalisar Kasar Somaliya

‘Yan Kunar Bakin Wake Sun Kashe ‘Yar Majalisar Kasar Somaliya

 

Akalla mutum 15, ciki har da wata ‘yar majalisar kasar Somaliya sun halaka, bayan da wasu ‘yan kunar bakin wake suka kai hare-hare biyu a garin Beledweyn na tsakiyar kasar.

Firaminista Mohamed Hussein Roble ya bayyana kashe Amina Mohamed Abdi a matsayin “kisan gilla”. Shi kuma shugaban kasar Abdullahi Farmajo ya aika da sakonsa na ta’aziyyar ta Twitter:

Cikin mamatan akwai tsohon dan majalisa Hassan Dhuhul da wasu sojojin Somaliya.

Kafofin yada labarai a yankin na cewa yawan mamatan na iya zarce alkaluman wadanda aka sanar a yanzu.

Babbar tashar talabijin ta Somaliya ta wallafa wasu hotuna na wadanda aka kashe yayin harin.

Kungiyar Al-Shabab ta dauki alhakin kai hare-haren – wadanda aka kai a biranen Mogadishu da tsakiyar Beledweyne.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp