Home Taska An Tsinci Gawar Jarumar Fim a Dakin Otel a Jahar Benue

An Tsinci Gawar Jarumar Fim a Dakin Otel a Jahar Benue

An Tsinci Gawar Jarumar Fim a Dakin Otel a Jahar Benue

Rundunar yan sanda na Jihar Benue ta tabbatar da cewa an tsinci gawar wata Takor Veronica a dakin otel a unguwar Nyinma.

Yan sanda sun ce an tarar da gawarta da tufafi kuma babu alamun rauni a jikinta wadda hakan na nuna akwai yiwuwar ba kashe ta aka yi ba.

Kakakin yan sandan Benue, Cathrene Anene ta ce a halin yanzu an kama mutum uku da ake zargi da hannu a mutuwar amma likitoci za su yi karin haske.

Jihar Benue – An tsinci gawar Jaruma Takor Veronica a cikin wani daki na Otel a Jihar Benue, kamar yadda The Nation ta rahoto.

A cewar rahotanni daban-daban, an gano gawar na Veronica ne kimanin sati baya bayan ta yi bikin zagayowar ranar haihuwarta.

An rahoto cewa an tsinci gawarta ne a wani dakin otel a unguwar Nyinma na Makurdi.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Benue, SP Catherine Anene ta tabbatar da afkuwar lamarin.

An kama mutane uku da ake zargi da hannu a kisar jarumar, Anene

Kakakin yan sandan ta ce an kama mutane uku da ake zargin suna da hannu a mutuwar jarumar.

“An kawo rahoton mutuwar wata mata a otel amma muna jiran bayani daga likitoci. Ba mu ga alamun rauni a jikinta ba. Don haka gwajin likitoci zai sanar da mu sanadin mutuwarta. Matar da ta mutu tana sanye da tufafi; ba mu ga alamar rauni a jikinta ba.

“An kama mutane uku da ake zargi da hannu a wannan, za su bamu karin bayani. Ba za mu iya cewa kashe ta aka yi ba domin ba mu ga alamar rauni ba,” in ji ta.

Abokanta da abokan aiki sun yi ta wallafa sakon ta’aziyya a dandalin sada zumunta.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp