Home SIYASA Kungiyar YBN ta kaddamar da Karin Reshe Uku a Tafiyar ta

Kungiyar YBN ta kaddamar da Karin Reshe Uku a Tafiyar ta

Kungiyar YBN ta kaddamar da Karin Reshe Uku a Tafiyar ta

Kungiyar tallata takarar shugabancin kasa ta Gwamna Yahaya Bello,wato Yahaya Bello Network (YBN) sun kaddamar da karin reshina guda 3 a karkashin kungiyar,wannan na zama karin azamar zurfafa kyakkyawar manufar tafiyar domin ganin hakar cimma ruwa bisa manufar siyaya a doron jagorancin Gwamna Yahaya Adoza Bello domin karbar Jagorancin kasar nan.

Kungiyar ta YBN tana kunshe da reshina guda bakwai mabambamta,Wanda kaddamar da guda uku a yanzu,jumullar su yazama guda goma.

Reshinan da aka kaddamar sun hada da reshen dalibai, da reshen mutane masu bukata ta musamman da Kuma ‘yan siyaya tun daga tushe.

A jawabin maraba daga bakin shugaban kungiyar Alhaji Abdurahman Muhammad Maikwashewa ya bayyana cewar manufar kungiyar ta YBN shine aiki tukuru wajen ganin Gwamna Yahaya Bello ya cimma muradansa a siyasace domin ganin cigaban kasa Nigeria, habbaka tattalin arziki,samar da ingantaccen tsaro, nagartaccen ilimi, kyakkyawan yanayi a harkar lafiya,dabbaka da’a da kuma tarbiyya.

Gwamna Yahaya Bello Wanda yasamu wakilcin shugaban ma’aikata na Jihar Kogi Jami’u Asuku, yayin dayake kaddamar da reshinan ya bayyana jin dadin sa,da gamsuwar sa bisa wannan tsari da kungiyar YBN tayi da zurfin tunani gami da kyakkyawan hange wajen zakulo wadannan sahun mutane a cikin al’umma domin bada gudunmuwa a cikin tafiyar.

Dayake zantawa da ‘yan Jarida Shugaban na YBN Maikwashewa ya bayyana cewar kaddamar da wannan Rassa na da nasaba da la’akari da muhimmancin da dalibai suke dashi wajen samar da kasa Abar alfahari,kazalika masu bukata ta musamman na da gudunmuwa mai yawa da zasu iya bayarwa a al’umma,a matsayin su na ‘yan kasa jawo su jiki a dama dasu a harkoki da fannoni da dama na rayuwa na da tasiri kwarai.

Daga nasu bangaren reshinan da aka kaddamar sun bayyana tsagwaron farin cikin su,kana sun bayyana cewar sun nemi su bada gudunmuwa a tafiyar ne,sabili da bayan hange mai nisa sun tuke magaryar aminta cewar Gwamna Yahaya Bello shine mafita ga matsalolin kasar nan.

Kwamishinoni da kusoshin gwamnati daga Jihar Kogi sun samu halartar taron tare manyan taurarin masana’antar shirya shirya fina finai ta Kannywood, ‘yan jarida da dubban mutane.

Daga cikin jihohin da aka kaddamar da reshinan sun hadar da Jihar Kano,Jigawa, Nassarawa,Sokoto,Yobe,Gombe,Kwara,Adamawa,Filato,Zamfara,Borno,Katsina,Benue, Abuja,Kebbi,Kogi da Kuma Taraba.

Matashin ‘Dan Jarida

Musa Sani Aliyu

24-03-2022

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp