Home SIYASA Babu Takarar da Zan Fito a 2023 – Babatunde Fashola

Babu Takarar da Zan Fito a 2023 – Babatunde Fashola

Babu Takarar da Zan Fito a 2023 – Babatunde Fashola

Ministan ayyuka da gidaje a Najeriya, Babatunde Fashola, ya ce babu takarar da zai fito a 2023 sai ta shugabancin gidansa.

Ƙungiyoyi da dama sun jima suna kira ga Fashola ya shiga tseren shugaban kasa, amma ya ce matarsa na ‘ya’yans na can suna jiransa.

A cewarsa da zaran wa’adin mulkin su ya ƙare a 2023, zai koma gida a jihar Legas ya huta.

Abuja– Ministan ayyuka da gidaje, Babatunde Fashola, yace ya shiga takarar shugaban ƙasa amma na gidansa.

Mai taimakawa shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, kan harkon Midiya, Tolu Ogunlesi, shi ne ya bayyana kalaman Ministan a wani rubutu a shafinsa na Twitter.

Ministan ya yi wannan furucin ne lokacin da manema labarai suka tambaye shi game da shirin da yake yi yayin da zaɓen 2023 ke gabatowa.

Da yake ba su amsa, Fashola ya ce:

“Ina neman takarar shugaba amma a gida na, Legas zan koma, matata da ‘ya’ya na na can suna jiran shugaban su. Dukkan ma su neman takara ina musu fatan Alkhairi.”

A kwanakin baya, yan Najeriya sun yaɗa jita-jitar cewa tsohon gwamnan jihar Legas ɗin zai shiga tseren takarar shugaban ƙasa a 2023.

Wasu ƙungiyoyin masoya sun fara karaɗe sassan Najeriya da yaƙin neman zaɓen Ministan, inda suka rinka kira gare shi da ya fito takarar kujera lamba ɗaya a Najeriya.

Amma Ministan ya musanta alaƙa da irin waɗan nan ƙungiyoyi dake goyon bayan cewa ya fito takara.

Fashola ya maida hankali kan sauke nauyin dake kansa

Hadimin ministan, Hakeem Bello, ya bayyana cewa Fashola ya maida hankali ne wajen sauke nauyin dake kan ma’aikatarsa kuma ba za’a raba masa hankali ba.

A jawabinsa ya ce:

“Mai girma Minista ya maida hankalinsa kacokan kan jagorantar tawagarsa na ma’aikatar ayyuka da gidaje domin sauke nauyin da shugaba Buhari ya ɗora musu.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp