Home SIYASA Babu Takarar da Zan Fito a 2023 – Babatunde Fashola

Babu Takarar da Zan Fito a 2023 – Babatunde Fashola

Babu Takarar da Zan Fito a 2023 – Babatunde Fashola

Ministan ayyuka da gidaje a Najeriya, Babatunde Fashola, ya ce babu takarar da zai fito a 2023 sai ta shugabancin gidansa.

Ƙungiyoyi da dama sun jima suna kira ga Fashola ya shiga tseren shugaban kasa, amma ya ce matarsa na ‘ya’yans na can suna jiransa.

A cewarsa da zaran wa’adin mulkin su ya ƙare a 2023, zai koma gida a jihar Legas ya huta.

Abuja– Ministan ayyuka da gidaje, Babatunde Fashola, yace ya shiga takarar shugaban ƙasa amma na gidansa.

Mai taimakawa shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, kan harkon Midiya, Tolu Ogunlesi, shi ne ya bayyana kalaman Ministan a wani rubutu a shafinsa na Twitter.

Ministan ya yi wannan furucin ne lokacin da manema labarai suka tambaye shi game da shirin da yake yi yayin da zaɓen 2023 ke gabatowa.

Da yake ba su amsa, Fashola ya ce:

“Ina neman takarar shugaba amma a gida na, Legas zan koma, matata da ‘ya’ya na na can suna jiran shugaban su. Dukkan ma su neman takara ina musu fatan Alkhairi.”

A kwanakin baya, yan Najeriya sun yaɗa jita-jitar cewa tsohon gwamnan jihar Legas ɗin zai shiga tseren takarar shugaban ƙasa a 2023.

Wasu ƙungiyoyin masoya sun fara karaɗe sassan Najeriya da yaƙin neman zaɓen Ministan, inda suka rinka kira gare shi da ya fito takarar kujera lamba ɗaya a Najeriya.

Amma Ministan ya musanta alaƙa da irin waɗan nan ƙungiyoyi dake goyon bayan cewa ya fito takara.

Fashola ya maida hankali kan sauke nauyin dake kansa

Hadimin ministan, Hakeem Bello, ya bayyana cewa Fashola ya maida hankali ne wajen sauke nauyin dake kan ma’aikatarsa kuma ba za’a raba masa hankali ba.

A jawabinsa ya ce:

“Mai girma Minista ya maida hankalinsa kacokan kan jagorantar tawagarsa na ma’aikatar ayyuka da gidaje domin sauke nauyin da shugaba Buhari ya ɗora musu.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp