Home Taska Dakarun Sojin K’asa Sun Hallaka Gawurtaccen ‘Dan Awaren IPOB/ESN Ejike da ‘Yan...

Dakarun Sojin K’asa Sun Hallaka Gawurtaccen ‘Dan Awaren IPOB/ESN Ejike da ‘Yan Bindiga Uku a Jihar Anambra

Dakarun Sojin K’asa Sun Hallaka Gawurtaccen ‘Dan Awaren IPOB/ESN Ejike da ‘Yan Bindiga Uku a Jihar Anambra

Dakarun rundunar sojin k’asan Najeriya da ke yankin Kudu maso Gabas sun samu nasarar hallaka gawurtattun y’an k’ungiyar aware ta IPOB/ESN hud’u a garin Ihiala da ke jihar Anambra. Tsagerun Wad’anda sun fito ne domin tilastawa al’ummar yankin zaman gida da farko, sun bud’e wuta ne kusa da gidan mai da ke garin Ihiala. Dakarun mu bayan samun bayanai ta kiran waya, sun mamaye yankin, inda suka bud’e wuta da fafatawa mai tsawo. Dakarun sun samu nasarar hallaka jagoran y’an awaren mai suna Ejike da sauran tsagerun uku.

Dakarun namu kuma sun k’wato Babur d’aya, da bindigogi biyu k’irar harbi ka ruga, harsasai 12 da tabar wiwi da kuma sauran kayayyaki da dama.

Haka kuma, an sami tsautsayi, inda motar dake d’auke dakarun mu ta samu had’ari inda muka rasa hafsa d’aya da soja d’aya. Sa’an nan sojojin mu biyu sun sami raunuka kuma suna samun kulawa a asbitin mu a yankin.

Bayan nuna matuk’ar juyayin mu na rashin jajirtattun dakarun mu, muna kuma kira ga al’umma da kuma sauran hukumomin tsaro da su bamu had’in kai ta han’yar samar da muhimman bayanai da zai taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin.

Birgediya Janar Onyema Nwachukwu
Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Sojin Kasan Najeriya
9 FABARAIRU 2022

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp