Home Taska Dakarun Sojin K’asa Sun Hallaka Gawurtaccen ‘Dan Awaren IPOB/ESN Ejike da ‘Yan...

Dakarun Sojin K’asa Sun Hallaka Gawurtaccen ‘Dan Awaren IPOB/ESN Ejike da ‘Yan Bindiga Uku a Jihar Anambra

Dakarun Sojin K’asa Sun Hallaka Gawurtaccen ‘Dan Awaren IPOB/ESN Ejike da ‘Yan Bindiga Uku a Jihar Anambra

Dakarun rundunar sojin k’asan Najeriya da ke yankin Kudu maso Gabas sun samu nasarar hallaka gawurtattun y’an k’ungiyar aware ta IPOB/ESN hud’u a garin Ihiala da ke jihar Anambra. Tsagerun Wad’anda sun fito ne domin tilastawa al’ummar yankin zaman gida da farko, sun bud’e wuta ne kusa da gidan mai da ke garin Ihiala. Dakarun mu bayan samun bayanai ta kiran waya, sun mamaye yankin, inda suka bud’e wuta da fafatawa mai tsawo. Dakarun sun samu nasarar hallaka jagoran y’an awaren mai suna Ejike da sauran tsagerun uku.

Dakarun namu kuma sun k’wato Babur d’aya, da bindigogi biyu k’irar harbi ka ruga, harsasai 12 da tabar wiwi da kuma sauran kayayyaki da dama.

Haka kuma, an sami tsautsayi, inda motar dake d’auke dakarun mu ta samu had’ari inda muka rasa hafsa d’aya da soja d’aya. Sa’an nan sojojin mu biyu sun sami raunuka kuma suna samun kulawa a asbitin mu a yankin.

Bayan nuna matuk’ar juyayin mu na rashin jajirtattun dakarun mu, muna kuma kira ga al’umma da kuma sauran hukumomin tsaro da su bamu had’in kai ta han’yar samar da muhimman bayanai da zai taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin.

Birgediya Janar Onyema Nwachukwu
Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Sojin Kasan Najeriya
9 FABARAIRU 2022

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp