Home Taska Dakarun Sojin K’asa Sun Hallaka Gawurtaccen ‘Dan Awaren IPOB/ESN Ejike da ‘Yan...

Dakarun Sojin K’asa Sun Hallaka Gawurtaccen ‘Dan Awaren IPOB/ESN Ejike da ‘Yan Bindiga Uku a Jihar Anambra

Dakarun Sojin K’asa Sun Hallaka Gawurtaccen ‘Dan Awaren IPOB/ESN Ejike da ‘Yan Bindiga Uku a Jihar Anambra

Dakarun rundunar sojin k’asan Najeriya da ke yankin Kudu maso Gabas sun samu nasarar hallaka gawurtattun y’an k’ungiyar aware ta IPOB/ESN hud’u a garin Ihiala da ke jihar Anambra. Tsagerun Wad’anda sun fito ne domin tilastawa al’ummar yankin zaman gida da farko, sun bud’e wuta ne kusa da gidan mai da ke garin Ihiala. Dakarun mu bayan samun bayanai ta kiran waya, sun mamaye yankin, inda suka bud’e wuta da fafatawa mai tsawo. Dakarun sun samu nasarar hallaka jagoran y’an awaren mai suna Ejike da sauran tsagerun uku.

Dakarun namu kuma sun k’wato Babur d’aya, da bindigogi biyu k’irar harbi ka ruga, harsasai 12 da tabar wiwi da kuma sauran kayayyaki da dama.

Haka kuma, an sami tsautsayi, inda motar dake d’auke dakarun mu ta samu had’ari inda muka rasa hafsa d’aya da soja d’aya. Sa’an nan sojojin mu biyu sun sami raunuka kuma suna samun kulawa a asbitin mu a yankin.

Bayan nuna matuk’ar juyayin mu na rashin jajirtattun dakarun mu, muna kuma kira ga al’umma da kuma sauran hukumomin tsaro da su bamu had’in kai ta han’yar samar da muhimman bayanai da zai taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin.

Birgediya Janar Onyema Nwachukwu
Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Sojin Kasan Najeriya
9 FABARAIRU 2022

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp