Home Taska Dakarun Sojin K’asa Sun Hallaka Gawurtaccen ‘Dan Awaren IPOB/ESN Ejike da ‘Yan...

Dakarun Sojin K’asa Sun Hallaka Gawurtaccen ‘Dan Awaren IPOB/ESN Ejike da ‘Yan Bindiga Uku a Jihar Anambra

Dakarun Sojin K’asa Sun Hallaka Gawurtaccen ‘Dan Awaren IPOB/ESN Ejike da ‘Yan Bindiga Uku a Jihar Anambra

Dakarun rundunar sojin k’asan Najeriya da ke yankin Kudu maso Gabas sun samu nasarar hallaka gawurtattun y’an k’ungiyar aware ta IPOB/ESN hud’u a garin Ihiala da ke jihar Anambra. Tsagerun Wad’anda sun fito ne domin tilastawa al’ummar yankin zaman gida da farko, sun bud’e wuta ne kusa da gidan mai da ke garin Ihiala. Dakarun mu bayan samun bayanai ta kiran waya, sun mamaye yankin, inda suka bud’e wuta da fafatawa mai tsawo. Dakarun sun samu nasarar hallaka jagoran y’an awaren mai suna Ejike da sauran tsagerun uku.

Dakarun namu kuma sun k’wato Babur d’aya, da bindigogi biyu k’irar harbi ka ruga, harsasai 12 da tabar wiwi da kuma sauran kayayyaki da dama.

Haka kuma, an sami tsautsayi, inda motar dake d’auke dakarun mu ta samu had’ari inda muka rasa hafsa d’aya da soja d’aya. Sa’an nan sojojin mu biyu sun sami raunuka kuma suna samun kulawa a asbitin mu a yankin.

Bayan nuna matuk’ar juyayin mu na rashin jajirtattun dakarun mu, muna kuma kira ga al’umma da kuma sauran hukumomin tsaro da su bamu had’in kai ta han’yar samar da muhimman bayanai da zai taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin.

Birgediya Janar Onyema Nwachukwu
Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Sojin Kasan Najeriya
9 FABARAIRU 2022

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp