Home SIYASA Shugaban (NITDA) ya Halarci Taron Karrama Mai Girma Gwamnan Jigawa:-

Shugaban (NITDA) ya Halarci Taron Karrama Mai Girma Gwamnan Jigawa:-

Shugaban (NITDA) ya Halarci Taron Karrama Mai Girma Gwamnan Jigawa:-

Mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), a yau ya halarci taron karrama mai girma gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar, (MON, MNI), wanda ƙungiyar cigaban ƙasar Haɗejia, (Haɗejia Ina Mafita Initiative) ta yi.

Taron ya samu halartar mai girma mataimakin gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi Ɗan Moɗi, da mai girma kakakin majalissar dokoki na Jihar Jigawa, Onarabul Idris Garba Kareka, da mai martaba sarkin Haɗejia, kana kuma shugaban majalissar sarakunan Jihar Jigawa, Dakta Adamu Abubakar Maje Haruna, (CON), da mai girma sanatan ƙasar Haɗejia, Barista Ibrahim Hassan Haɗejia, (Shatiman Haɗejia Na Biyu), da mai girma tsohon shugaban hukumar kula da shige da fice ta ƙasa, (NIS), Alhaji Muhammad Babandede,

Sai kuma ƴan majalissar wakilai na tarayya da ƴan majalissar dokokin Jiha, da shugabannin ƙananan hukumomi da sauran muhimman mutane da dama na ƙasar Haɗejia da Jigawa.

Daga bisani kuma kafin ya komawa birnin tarayya, Abuja, mai girma shugaba ya karɓi baƙuncin al’umma daban-daban, dattawa, matasa, da kuma ƴan ƙungiyoyi, waɗanda su ka haɗa da: ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyi magoya bayan shugaban ƙasa Malam Muhammadu Buhari, (GCFR), “Coalition Of Buhari Support Groups”, (COBSG), ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙungiyar, Onarabul Musa Gambo Guri, waɗanda su ka kai masa ziyarar girmamawa tare da godiya a bisa wakilci da ya aike wurin babban taron ƙungiyar na shiyar Arewa Maso Yamma da aka yi a Jihar Jigawa.

Kana kuma, ya karɓi baƙuncin wasu daga cikin matasan da su ka samu horo kan ilimin gyaran wayar salula da sauran harkokin fasaha na zamani wanda hukumarsa ta gudanar a kwanan nan, inda su ka ziyarce shi domin yi masa godiya da yabawa kan ƙoƙarin da ya ke wajen ɗora rayuwar matasa kan harkar cigaba domin bunƙasa cigaban ƙasa da duk al’umma.

Lahadi, 6 ga watan Janairu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp