Home SIYASA Shugaban (NITDA) ya Halarci Taron Karrama Mai Girma Gwamnan Jigawa:-

Shugaban (NITDA) ya Halarci Taron Karrama Mai Girma Gwamnan Jigawa:-

Shugaban (NITDA) ya Halarci Taron Karrama Mai Girma Gwamnan Jigawa:-

Mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), a yau ya halarci taron karrama mai girma gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar, (MON, MNI), wanda ƙungiyar cigaban ƙasar Haɗejia, (Haɗejia Ina Mafita Initiative) ta yi.

Taron ya samu halartar mai girma mataimakin gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi Ɗan Moɗi, da mai girma kakakin majalissar dokoki na Jihar Jigawa, Onarabul Idris Garba Kareka, da mai martaba sarkin Haɗejia, kana kuma shugaban majalissar sarakunan Jihar Jigawa, Dakta Adamu Abubakar Maje Haruna, (CON), da mai girma sanatan ƙasar Haɗejia, Barista Ibrahim Hassan Haɗejia, (Shatiman Haɗejia Na Biyu), da mai girma tsohon shugaban hukumar kula da shige da fice ta ƙasa, (NIS), Alhaji Muhammad Babandede,

Sai kuma ƴan majalissar wakilai na tarayya da ƴan majalissar dokokin Jiha, da shugabannin ƙananan hukumomi da sauran muhimman mutane da dama na ƙasar Haɗejia da Jigawa.

Daga bisani kuma kafin ya komawa birnin tarayya, Abuja, mai girma shugaba ya karɓi baƙuncin al’umma daban-daban, dattawa, matasa, da kuma ƴan ƙungiyoyi, waɗanda su ka haɗa da: ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyi magoya bayan shugaban ƙasa Malam Muhammadu Buhari, (GCFR), “Coalition Of Buhari Support Groups”, (COBSG), ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙungiyar, Onarabul Musa Gambo Guri, waɗanda su ka kai masa ziyarar girmamawa tare da godiya a bisa wakilci da ya aike wurin babban taron ƙungiyar na shiyar Arewa Maso Yamma da aka yi a Jihar Jigawa.

Kana kuma, ya karɓi baƙuncin wasu daga cikin matasan da su ka samu horo kan ilimin gyaran wayar salula da sauran harkokin fasaha na zamani wanda hukumarsa ta gudanar a kwanan nan, inda su ka ziyarce shi domin yi masa godiya da yabawa kan ƙoƙarin da ya ke wajen ɗora rayuwar matasa kan harkar cigaba domin bunƙasa cigaban ƙasa da duk al’umma.

Lahadi, 6 ga watan Janairu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp